advanced Search
Dubawa
6499
Ranar Isar da Sako: 2016/05/10
Takaitacciyar Tambaya
shin a ina kaburburan wasu annabawan suke irin su annabi shu’aibu, ludu, yusuf, yunus, ibrahim? Yaya suka rasu? Shin kowannensu yana da harami da hubbare?
SWALI
Don Allah ku amsa mun wadannan tambayoyin: 1-amsa a dunkule: Shin a ina kaburburan wasu annabawan suke kamar su annabi Shu’aibu, Ludu, Yusufu, Yunus, Adamu, Musa, Isma’il, Ishak, Ibrahim, Harun, Dawud, Sulaiman, Isa, Yahya, Zakriya Da Nuhu Kur’ani (a.s)? 2- yaya mutuwar kowannensu ta kasance? Kur’ani Shin kowannensu yana da harami da hubbare. ?
Amsa a Dunkule
Kusan akwai sabani tsakanin malaman tarihi a kan batutuwa masu yawa da suka Shafi tarihi, kamar bayanin Kur’ani yadda rayuwar wasu muhimmam mutane ta gudana, musaman annabawan Allah, sai dai kalilan daga cikinsu, akwai wadanda da babu wasu kafafe na tarihi da suka kawo tabbataccen bayani game da rayuwarsu da yadda suka yi wafati da gurin da aka binne su.
Sai dai abin da ya inganta a kafafen tarihi na daga tarihin annabawa -in ban da Annabin Musulunci (s.a.w)- shi ne; Annabi Ibrahim (a.s) kabarinsa yana garin Khalil a kasar Falasdinu da aka mamaye, yana da hubbare da harami. Annabi Nuhu da Annabi Adamu (a.s) an binnesu ne a garin Najaf dake kasar Iraki a nan hubbaren Imamu Kur’ani Ali (a.s). Annabi Musa da Annabi Haruna (a.s), an binnesu ne a saharar Taiha. Annabi Daniyalu (a.s), kabarinsa na jahar Khurdistan a garin Shush a kasar jamhuriyar Musulunci ta Iran. Haka shi ma Annabi Kaida’ar Kur’ani (a.s) kabarinsa na jahar Zanja’an a Kur’ani jamhuriya Musulunci ta Iran.
 
Amsa Dalla-dalla
Ya dace mu bayyana mahimman abubuwa kafin amsa wannan tambayar:
 1- Kusan akwai sabani tsakanin malaman tarihi a kan batutuwa masu yawa da suka Shafi tarihi, kamar batun yadda rayuwar wasu muhimmam mutane ya gudana, musaman annabawan Allah, sai dai kalilan daga cikinsu, akwai wadanda babu wasu kafafe na tarihi da suka kawo tabbataccen bayani game da rayuwarsu da yadda suka yi wafati da gurin da aka binne su. Sai dai kasntuwar tahirin annabawa tushensa ya faro ne tun farkon tarihin bil Adama, wannan wani bangare ke nan. Amma a daya gefen idan zamu waiga Kur’ani kundin tarihi da bai dade fiye da rubu’in kani na rayuwar bil Adama ba a Duniya, ko kasa da haka sosai, don Kur’ani kusan an yi watsi da kaso mai yawa na tarihi da ba a rubuta ba na abubuwan da suka faru.
Wani lokacin a kan rubuta amma sai ya lalace saboda tsawon zamani ko sakaci ko bisa wasu dalilai na daban. Misali, ambaliyar ruwa, girgizar kasa, yake-yake, hare-hare, zagon-kasa, bacewar kayayykin tarihi, mamayar wasu al’adun wasu kasashe da sauran su.
2- Abin da aka samu kan abin da ya shafi tarihin annabawa (a.s) duk annabawan da Allah (s.w.t) Ya aiko, sun zo ne da nufin ceto bil Adama ne da shiryar da shi zuwa ga Allah da yawansu ya kai annabawa 124000. Kur’ani Mafi akasari ba a ambacesu a tarihi ba, kuma tarihi bai ambaci wani abu game da rayuwarsu da mutuwarsu da Shahadarsu da inda aka binne su, kai koma sunayensu ba a kawo ba.
 3- Sai dai duk da haka akwai bayanai karbabbu kan tarihin rayuwar wasu annabawan. Sai dai abin da ya karbu a kafafen tarihi na daga tarihin annabawa -in ban da Annabin Musulunci (s.a.w)- shi ne cewa Annabi Ibrahim (a.s) kabarinsa yana garin Khalil a kasar Falasdinu da aka mamaye, yana da hubbare da harami. Akwai tarihin da ke nuna cewa Annabi Nuhu da Annabi Adamu (a.s) an binne su ne a garin Najaf a kasar Iraki anan hubbaren Imamu Kur’ani Ali (a.s). Annabi Musa da Annabi Haruna (a.s), an binne su ne a saharar Taiha[1]. Annabi Daniyalu (a.s), kabarinsa na jahar Khurdistan a garin Shush a kasar jamhuriyar Musulunci ta Iran. Haka shi ma Annabi Kaida’ar kabarinsa (a.s), jahar Zanjan a kasar Kur’ani jamhuriyya Musulunci ta Iran. Shi kuma Annabi Haikuk Kur’ani (a.s) kabarinsa na Tusrika’an, Annabi Zulkifli yan wani yankin Basima da ke Iraki da[2].
4- Abin da ya dace mu yi nuni a nan shi ne; Kur’ani kowane musulmi ya sani game da annabawa Kur’ani (a.s) shi ne, tilas ya yi imani da annabcinsu da aikensu. Kur’ani Sanin fiye da hakan ba wajibi ne; kamar tarihin haihuwarsu da kuma Kur’ani wafatinsu da…, Kamar yadda Kur’ani ke hanunka mai sanda babu amfanin Kur’ani bayayyana komai dalla-dalla[3]. Abin da ya fi shafarmu da zai amfane mu shi ne koyarwarsu, wadda aka tsara ta kyakkyawar fuska da kamala mafi kyau, na tsarin karantarwar Annabi Muhammad. Kazalika ya dace mu san wahalhalu da matsaloli da kuntata da annabawan suka fuskanta, da yadda suka jure suka wahala a gun tunkarar jagororin kafurci da shirka ta yadda suka isar da sakon Allah zuwa ga jama’a, duka abubuwa masu kyau da Kur’ani suka fi dacewa, mu sani da darussa da ke cikn tarihin rayuwarsu[4].
 

[1] Akwai sabani tsakanin masu hadisai da malaman tafsiri kan wasu kan ce a saharar Saina’a kusa da Baitul mukddas, ko garin Ariha ya ke. Amma wasu cewa suke yana nan tsakanin Falasdinu da Masar. Mafi yawan masana Kur’ani sun ce yana nan tsakanin Falasdinu da Iblu da Jodan akwai Kur’ani tazarar farsakhi shida. Sai a dubi tafsarai aya 26 Ma’ida.
[2] Domin samun karin bayani dangane da wasu annabawan kamar Annabi Ibrahim, Musa, Isa, Nuhu da Adamu Kur’ani (a.s). Sai ku dubi shfin yanar gizo na islam. com, da wasu littatafai kamarsu Hayatul kulub na Allama Maslisi, Tarikhul anbiya. a na Sayyid Hashim Rasuli Mala’e da Shafin Shafin Gadir a yanar gizo.
[3] Labarin Kur’ani Mai Girma na AShabul Kahfi na kara tabbar da bayanammu, inda ya ke cewa: “Suna cewa uku ne karensu na hudunsu, suna cewa biyar ne karensu na shidansu, lalube a duhu. suna bakwai ne natakwasdinsu karensu. Ka ce Ubangijina ne Ya san adadinsu, babu wanda suka san su sai yan kadan. Kada ka yi jayayya da su sai jayayya ta zahiri, kada ka tambayi wani daga cikinsu” Kahfi: 22.
[4] Hakika ya kasance cikin kissarsu akwai izna ga ma’abuta hankali, ba labara ba ne da aka kirkira sai Kur’ani gaskatawa ga abin da ke gunsa da kuma bayanin komai, kana shiriya da rahama ga muta ne masu imani, Yusuf 111.
TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

Mafi Dubawa