advanced Search
KAGUA
6084
Tarehe ya kuingizwa: 2012/08/16
Summary Maswali
Shin aure yana da wasu sharaDai na musamman?.
SWALI
Shin aure na da wasu sharaDai na musamman? Kuma shin idan mace da namiji sun yarjewa kansu da juna, (duk da haka) akwai buKatar su karanto matani sigar Daura auren wani lokaci?
MUKHTASARI WA JAWABU
A mahangar musulunci auren da’imi da na mutu’a suna da sharaDai waDanda sune kamar haka:-
1.             Karanto siga (Yarjewa juna tsakanin miji da mata shi kaDai bai wadatar ba lalle ne a hada shi da furta “farar da” lafazi na musamman).
2.             Bisa ihtiyaDi na wajibi ya zama dole a karanta sigar Daura aure da harshen larabci ingantacce, idan kuma mijin da matar ba za su iya karanto sigar da larabci daidai ba ya inganta su karanta ta da ko wane yare. Bai zama dole su sanya wakili ba, amma wajibi ne su karantao lafazin da a fahimci cewa ya ba da ma’anar “na aurar maka” da “na kaba”. (ma’ana lafazin da ma’anarsa ta yi daidai da “na aurar maka” da “na kaba”).
3.             Idan miji da mata suka karanto sigar aure, a aure na da’imi, matar za ta fara cewa: “zauwajtuka nafsi alas sadaKil ma’alum” (na aura maka kai na bisa sadaKi sannane) daga nan ba tare da jira ba sai milin ya ce: “Kabiltut tazwij” (na karbi auren), auren ya yi, ya inganta, idan kuma wani daga cikinsu ya sanya wakili ya karbar masa wauren, idan ya zama bisa misali sunan mijin Ahmad ita kuma matar sunanta faDima, shi wakilin matar zai ce: “zauwajtuka muwakkilati FaDima muwakkilaka Ahmad alas sadaKil ma’alum” (na aurar da wacce ta wakilta ni faDima ga wanda ya wanda ya wakilta ka Ahmad disa dakaKi sananne), ba tare da jinkiri ba sai wakilin mijin ya ce ”Kabiltu li muwakkili Ahmad alas sadaK” (na karBarwa wanda ya wakilta ni Ahmad bisa sadaKin), idan suka yi haka auren ya inganta.  
Amma sigar Kullar auren wani lokaci bayan da aka ayyana lokaci da sadaKi, sai matar ta ce: “zauwajtuka nafsi fil muddatil ma’aluma alal mahril ma’alum” (na aura maka kaina a cikin tsawon lokaci sannane bisa dadaKi sananne).
Bayan wannan ba tare da jinkiri ba sai mijin ya ce: “Kabiltu” (na karba). Da wannan Auren ya Kullu kenan. Ko kuma wakilin matar ya ce da wakilin mijin: “matta’atuka muwakkilati muwakkilaka fil muddatil ma’aluma” (na aurar da wacce nake wakilta (auren wani lokaci) ga wanda kake wakilta a cikin sanannen lokaci bisa sadaKi sananne), sai wakilin matar ba tare da jinkirtawa ba ya ce: “Kabiltu limuwakkili hakaza” (na karBawa wanda na ke wakita bisa yadda ka fada). Idan suk yi haka auren ya inganta.  
4.             A ayyana sadaki kuma a fade shi a wajen daurin auren. 
5.             Wanda ya furta Kalmar daurin auren mijin ne ko matar ko kuma wakilinsu ya zama dole ya yi nufin afkarwa ko fararwa yayin furtawar, ma’ana idan su kansu mijin da matar ne suka furta sigar auren sai matar ta ce da mijin “zauwajtuka nafsi” da nufin cewa daga yanzu ya zama mijinta shi ma mijin ya ce: Kabiltut tazwij” da nufin daga yanzu ya karBe ta a matsayin matarsa.
6.             Wanda zai furta sigar aure ya zama baligi mai hankali.
7.             Idan wakilin mace ne zai furta siga a wajen Daura aure lalle ne ya faDi sunan wanda yake wakilta, haka ma wakilin miji.
8.             Yarinyar da ta isa ta zama baliga mai cikaken hankali da ta san maslahar kanta (rashida), idan tana son yin aure mutuKar dai budurwa ce zata nemi izinin babanta ko kakanta, amma idan ba budurwa ba ce, idan ya zama ta rasa budurci ta a sakamakon auren da ta yi a baya, ba dole ne sai ta nemi izinin uba da kaka ba.
9.             A yayin da mace ke yin sabon aure, lalle ne kar matar ta zama tana da wani aure na da’imi ko na wani lokaci a kanta, kuma kar ta kasance a cikin kwanakin iddar aure na da’imi ko na wani lokaci.
10.          Aure ya zama bisa yardar matar da mijin kuma lalle ne kar ya zama bisa fin Karfi da tilastawa[1].
11.          Idan mace na so ta auri wani mutum idan a baya ta auri wani sai ya sake ta ko kuma lokacin auren (da ta yi na wani lokaci) ya Kare to lalle ne ya zama kwanakin iddar ta ma sun kare.
12.          Wani sharaDi shi ne, dole ne ya zama a lokacin da matar ta ke da aure a baya ba ta yi zina da wanda take so ta aura a yanzu ba, don haka idan mutum ya yi zina da matar da ke da miji to ta haramta a gare shi har a bada[2].
Wannan shi ne abin da aka naKalto bisa fatawar Imam Khomaini (ra) kuma waDannan su ne sharaDan aure a dunkule, wanda yake son samun Karin bayani ya koma wa litattafan fiKihu da na fatawoyi maraji’ai. Idan kuma kana son fatawar wani mar’ja’i na musamman, to ka kuma rubuto mana wasiKa tare da ambaton sunan mar’ja’in.   
A kowane hali amsar mai girma ayatollah Mahdi Hadawi Tahrani (Allah ya tsawaita rayuwarsa) a Bangare na biyu na tambayar da ka yi shi ne: duk wata alaKa ta sha’awa da aka kulla tsakani mace da namiji ba tare da aure na da’imi ko na wani lokaci ba haramtacciya ce, kuma yardar zuciya ko yarjewa juna da amincewa ba sa isarwa wajen tabbatar da aure.
MahaDar site din fatawoyi

[1] Imam Khomaini sayyid Ruhullah a cikin taudhihul ma’sa’il din marja’ai j 2 shafi 449 zuwa 460, daftari intsharat islami Kum, bugu na takwas 1424. Da tahrirul wasila j 2 shafi ba 710  da kuma shafi na 734 zuwa 736.
[2] An cirato daja jigo na 961 (yin wani auren bayan yin auren wani lokaci)
TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
MAONI
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
mfano : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
<< Niburute.
Tafadhali ingiza kiasi sahihi ya usalama Kanuni

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

MASWALI KIHOLELA