advanced Search
Dubawa
11884
Ranar Isar da Sako: 2012/05/05
Takaitacciyar Tambaya
Me ake nufi da Kalmar Rayuka, wadda ta zo a cikin Ziyarar Ashura? “Aminci ya Tabbata a gare ka ya Baban Abdullah da Rayukan da suka Sauka a Farfajiyarka”
SWALI
Me ake nufi da Kalmar Rayuka, wadda ta zo a cikin Ziyarar Ashura? Aminci ya Tabbata a gareka ya Baban Abdullah da Rawukan da suka Sauka a Farfajiyarka” Shin ana nufin Rawukan wadanda suke zuwa Ziyarar Imam ne? ko ana nufin Rawukan wadanda aka Bisine su a karbala kusa da shi? Ko Wadanda suka ba da Rayuwarsu ga Imam Husain, suka Sadaukar da Rayuwarsu a Hanyar Imam, (Sahabban Imam Husain)?
Amsa a Dunkule

 Abin da ake nufi da Kalmar ”Rawukan da suka sauka a Farfajiyarka” su ne Shahidai, wadanda suka yi Shahada tare da Shugaban Shahidai (A.s) a Filin Karbala.

Wadannan su ne Dalilan da suke Tabbatar da haka;

  1. A bisa Al’ada masu Ziyara wadanda suke da Rai ba a Kiransu da Sunan arwah. (Rayuka)
  2. Ita wannan Ziyara Zance ne daga wanda ya kawo Ziyara, a bisa Al’ada ba zai Zamo da mai Zance da wanda ake Zance da shi, a kira su da suna Daya ba.
  3. Dukkan Addu’o’in Ziyara da aka ruwaito ga Imam Husain (A.s) babu yin Sallama ga masu kai Ziyara Gare shi.
  4. An Ruwaito Ziyarar Ashura ne tun Kafin a Bisine Wadanda suke Kwance na yanzu a wurin, wannan ya nuna kenan, Kalmar Rayuka ba ta Nufin dukkan Wadanda suke Kwance a wurin.
  5. Daga cikin Kalmomin Shaidu da ke cikin wannan Ziyara zamu iya Fahimtar cewa Kalmar Rawukan Wadanda ake musu Sallama, su ne Shahidai wadanda suka yi Shahada tare da Shugaban Shahidai a Filin Karbala, domin yazo a cikin wani wurin, za’a yi Sallama ta Musamman ga Wadanda suke tare da Imam: (Amincin Allah ya Tabbata ga Husain da Ali Dan Husain da Yayan Husain da Sahabban Husain”

Kuma Kari aka haka shi ne cewa ai Ita Ziyarar Ashura, a Dunkule ta Kunshi yin Sallama ne ga Shugaban Shahidai da “ya” yansa da da Sahabbansa, da kuma bayyana so, da cika Alkawari ga Imam, da kuma Nesantar Makiyansa.

  1. Yazo a cikin wata Ziyara ta Ashura, Kalmar da take cewa: Amincin Allah ya Tabbata a gare ka da kuma Rawukan wadanda da suka sauka a Farfajiyarka, (Hallat da Anakhat) suka yi Jihadi don Allah a tare da kai, suka sayar da rawukansu don Neman Yardar Allah a cikin al” amarinka[1] Acikin wannan Jumlar wasu Suffofi sun Fito, irin su yin Jihadi a Hanyar Allah, tare da Shuigaban Shahidai (as) da yin Shahada don neman Yardar Allah tare da Shugaban Shahidai.Wadannan Siffofi sun zo ne bayan Siffanta su da Kalmar (Hallat da Anakhat) wato Sauka a Farfajiyar Shugaban Shahidai (as)

 daga wadannan Kalmomi za a Fahimci cewa[2] Kalmar Rayuka da a ke nufi shi ne Rawukan Shahidai Wadanda suke tare da Shugaban Shahidai.

  1. Yazo a cikin wata Addu’a ta Ziyarar Ashura, banda waccan da ta Shahara[3] Ana cewa: Amincin Allah ya Tabbata a gareka, ya Baban Abdullah Al Husain, da wadanda suka taimaka maka suka ba da taimako, suka Tayaka da Kawukan su, suka Mika Wuyayen su a wajen Kariya gareka, ….Aminci ya tabbata a gareka ya Shugaba na, (Aminci ) ya tabbata a gare su , da Ruhinka da Ruhinsu da Turbarka da Turbarsu , Aminci ya tabbata a gareka, ya dan Shugaban Halittu, da wadanda suka yi Shahada a Tare da kai.

 Daga wadan nan kalmomi za’a iya fahimta a fili cewa Kalmar rawukan da ake                    nufi su ne shahidan da suka yi shahada a tare da shugaban shahidai.

  1. Yazo a cikin wata Ziyara ta Shugaban Shahidai (as) Bayan an Karanta Ziyarar Imam Husain da Aliyyul Akbar (AS) sai a Fuskanci Shahidan Karbala a karanta wannan Ziyarar…….kuma Zamowar a cikin Dukkan Addu’o’in Ziyarori ga Shugaban Shahidai, babu yin Sallama ga masu Ziyara ko ga Wadanda aka Bisne su a wurin, zamu samu Natijar cewa abisa la’akari da Gamammiyar addu’o’in Ziyarori na Ashura da sauran Ziyarori na Shugaban Shahidai, ba tare da wani Kokwanto ba zamu iya cewa Kalmar Rawukan da ake Sallama a gare su Acikin Ziyarar Ashura su ne Shahidan da suke tare da Shgugaban Shahidai (as) (a lokacin shahadarsa).

 


[1] Sayyid Ibn Tawus, Ikbalul A’mal Juzu’i 3 Shafi-70

[2] Itace Ziyarar da take da irin Ladar Ziyarar Ashura, ga wanda ba zai iya yin dukkan Ladubban Ziyarar Ashura ba (na yin Kabbara da La’anta 100 da yin Sallama 100 da yin Sujuda da Sallah da yin Addua bayan ziyara) Mafatihul Jinan.

[3] Za’a iya Fahimtar hikimar Jinkirta Fadin Kalmar yin Jihadi da Shahada, sai bayan an Ambaci Kalmar (Hallat da Anakhat) Wadanda suke nufin Sauka, cewa Kalmar Rayuka na nufin Shahidan da suka yi Shahada a Ranar Ashura A tare da Shugaban Shahidai (as) .

 

TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

  • Me ake nufi da hadisi rafa’i
    13131 مبانی فقهی و اصولی 2012/07/26
    An rawaito hadisi rafa’i daga manzo (s.a.w) da kamanni biyu, daya ya kunshi shari’a da wajabcinta ko daukakar lamarinta kan mutum kamar na aikin da ke kan kowane baligi cikin mutane, na addinin musulunci, a daya bangaren kuma hadisi rafa’I, girman nauyin shari’a wato takalifin hukunce hukuncen ...
  • Shin shedan na da zuriya, kuma shin su ma la'anannu ne?
    8301 ابلیس و شیطان 2012/07/24
    Hakika shedan na da zuriya kuma su ma la'anannu ne kamar yadda yake la'ananne, domin su ma bisa hakika sun bi tafarkin sa kuma sun yi riko da hanyarsa da salonsa wajen batarwa da kokarin kautarwa daga tafarkin gaskiya, sun dogara da wannan hanyar a wajen batar ...
  • Me ake nufi da akwati wadda aka fada cikin hadisin ghadir da Manzo (s.a.w) ya ce a bawa imam Ali (a.s)?
    4236 Dirayar Hadisi 2019/06/15
    Lafazin akwati yazo cikin wani bangaren hadisi da mai littafin bihar ya rawaito, hakan yazo cikin fadinsa madaukakin sarki “hakika alamar mulkinsa ita ce akwati da zai zo muku dashi, acikinsa akwai nutsuwa daga ubangijinku”, wasu daga malaman tafsiri sun fassara ma’anar akwati da cewa ita ce ...
  • Me ye alaka tsakanin Zuhudu da ci gaban zamani?
    9449 Halayen Nazari 2012/07/24
    Kalmar zuhudu da saukin rayuwa suna daga kamalar halaye, wanda ya koma zuwa ga littattafanmu na shari'a zai samu cewa sun muhimmantar da wannan kalma da yawa, kuma sun karfafa ta sosai, suna masu nuni da kwadaitarwa da rashin damfaruwa da duniya da adonta, sai dai abin ...
  • Wadanne Ne Mafi Mihammancin Hakkokin Zamantakewa A Matakin Kasa Da na Jaha A Mahangar Imam Ali (a.s)?
    2688 روایات و دعاهای برجای مانده 2019/10/09
  • mene ne hanyar debe kewa da Kur’ani
    9347 Halayen Aiki 2012/07/25
    idan ya zama tilawar da mutum zai yi ta Kur’ani don neman kusanci ne zuwa ga Allah, da tadabburi da bibiyar aiki da shi, to zai zama tilawar ta kusantar da shi ga manufar Kur’ani sosai, zai zama son Kur’ani zai tsananta. ...
  • Shin ruwan maziyyi, waziyyi da wadiyyi najasa ne?
    6808 Hakoki da Hukuncin Shari'a 2020/05/19
    ruwan da yake fita daga jikin dan adam idan aka cire Bawali da Maniyyi ya kasu kamar haka:Na daya: Ruwan da yake fitowa bayan bawali kuma yana da danko kadan wanda ana kiransa Madiyyi.Na biyu: Ruwan da yake fita yayin jjin ...
  • mene ne gwargwadon tasirin Allah madaukaki a rayuwar mutum?
    9111 Irfanin Nazari 2012/07/25
    Ba yadda za a wani aiki ya fita daga iradar Allah mai hikima, wannan iradar ta Allah tana nan a ko da yaushe a rayuwar mutum a kowane lokaci da zamani, da dukkan dokokin rayuwa ba tare da ta cire wa mutum zabin da yake da shi ...
  • menene abin sha mai tsarkakewa?
    16145 شراب طهور 2012/09/16
    "Ashsharab" abin nufi duk abin sha "Addahiru" abin nufi mai tsaki mai tsarkakewa wannan kalma an yi amfani da ita a cikin ayoyi daban-daban a gidan aljanna ana samun abin sha mai tsarki mai dadi iri-iri mai yanayi kala-kala, hakika Kur'ani mai girma ya kawo maganar sa ...
  • Shin hadisin da ke cewa: “Mutane (musulmi) zasu rbu zuwa bangarori saba’in da uku (73)” ingantacce ne kuwa?
    5044 Dirayar Hadisi 2019/06/15
    Malaman hadisi daga sunna da shi’a sun kawo hadisin “rabuwar mutane” ta bangarori masu sabawa juna. Kuma dukkan wadannan hadisai da Shi’a, sunna suka kawo yana labarto rabuwar musulmai bayan manzo (s.a.w), ruwaya ce a yadda take, idan zamu dauki daya daga ruwayoyin Shi’a daga wadannan hadisai ...

Mafi Dubawa