A zamanin boyuwar Imam Mahadi (a.s) "jagorancin malami" wani asasi ne tabbatacce kuma doka gama gari ta duniya wacce take daga tsarin siyasar musulunci, kuma matsayin malami dole ne ya kasance a matsayin jagora a matsayin shugaba mai yanke hukunci da bayar da umarni kuma ya kasance ...
Wannan hadisin babu shi a cikin littattafan Shi'a, sai dai cewa wsu daga malamai sun yi nuni da shi. Wannan hadisin an same shi a littattafan ahlussunna ne kawai a littafin sunan Abu Dawud (wanda yake daga manyan littattafan hadisin Sunna) kuma bisa zahiri wasu sun nakalto ...
A cikin Kur'ani mai girma muna karanto wannan ayar {lalle ba ku yake su ba, sai dai Allah ne ya yake su kuma Ba kai ne (ya kai wannan Annabi) ka yi jifa ba (a lokacin da ka jefe su da kasa da duwatsu) a lokacin da ...
Lallai babu shakka Imam Husaini (a.s) yana da wasu baye-baye na masamman. Kamar kasantuwarsa baban Imamai (a.s) wadanda dukkansu sun biyo ta tsatsonsa ne (a.s). Ana samu waraka ta hanyar Turbarsa, da karbuwar Addu'a a Hubbarensa mai daraja. Amma duk da wannan karamomi da kebantattun darajoji, ba ...
Babu wani kokwanton cewa Allah (s.w.t) ya san komai, kuma a kowane hali, kuma babu wata ma’ana ga boye wa Allah wani abu, haka nan Allah (s.w.t) ba shi da hukuncin namiji ajnabi game da mace yayin addu’a? sai dai yayin ibada mutum yana samun kansa a ...
Kasancewar Sayyida Fatima (a.s) ta yi shaukin ganin Salmanul Farisi hakan ba shi da wata matsala da ma’asumancinta saboda da za ka lura da farkon hadisin da ma karshensa zaka fuskanci cewa wannan haduwa da su ka yi ta kasance bayan wafatin manzon Allah (s.a.w) sannan zaka ...
Dangantaka tsakanin malaman Shi’a da mahukuntan daular Safawiya da ma mahukunta na wasu dauloli da nufin raunana Shari’a ba ne. Dalilan yin hakan su ne samar da mamora da kyakkyawan manufa ga al’umma da yin wannan alakar kan haifar don taimakon jama’a da yada Mazhabar Shi’a da ...
Kur'ani ya zo da salon bayani kala-kala dangane da halittar Adam amincin Allah ya tabbata a gare shi wanda za a iya fahimtar cewa halitta Adam amincin Allah ya tabbata a gare shi ta kasance bisa wasu matakai mabanbanta daya bayan daya, kamar yadda zai zo:
Abin da zamu kawo a dunkule shi ne msar tambayar. Hakika Kur'ani tushe ne daga tushen shari'a, kuma shi ake komawa don gane ra'ayin addini. Ba hakan nan ake istinbadi da Al-Kur'ani ba sai abubuwa biyu sun tabbata: kafa dalilin tabbatar da Al-Kur'anin, sannan ...
Mas'alar jagorancin malami a matsayin shugaban al'umma a musulunci wani hakki ne da aka sanya shi ga wanda ya kai matakin ijtihadi. Wasu suna ganin lamari ne sabo a cikin fikirar musulunci, sai dai jagorancin malami a matsayin wani umarni na mai shari'a mai tsarki a lokacin ...
Daga tarin ayoyi da ruwayoyi da kuma tafsire zamu iya anfana da cewa a cikin lamarin kisan kai da annabi halliru ya aikata wato kashe yaro matashi, ba ya aikata hakan bane domin son rai da fushi ba, sai dai dan yana da tabbacin cewa a cikin ...
Duk da yake Annabin Musulunci wanda shi ya fi girma, shi ne mafificin Annabawa, kuma mafi daukakar daraja, to amma wannan Hususiyar tasa (wato girman da ya kebantu da ita) bai zamo wajibi ya zamo dole sai ya tattaro dukkan kebance-kebancen dukkan Annabawa da Manzanni ba, a ...
Abdulqadir Jilani da ake yi wa laqabi da gausul a’azam shi masani ne sufi da aka haife shi a arewacin iran a qarni na biyar, wanda ya mutu a bagdad a qarni na shida. Amma alaqarsa da imam Sadiq (a.s) da savawarsa gare shi to ...
kafin mu Amsa wannan tambayar yana da kyau a san cewa, su ruwayoyi gaba dayansu, za a iya kasa su kashi biyu, kashi na farko, anace musu ingantattu masu karfi… Akwai kuma wani kashin na ruwayoyi, wadanda ake ce musu raunana, wadanda ba za a iya jingina ...
Mafarki wani al’amari ne dake faruwa ga dukkan mutane (a cikin barcinsu) a tsawon rayuwarsu. Sai dai har yanzu malamai ba su iya samun cikakkiyar saninsa ba da yadda yake faruwa. Al’kar’ani mai girma ya bamu labarin Annabi Yusuf (a.s) game da mafarkinsa na gaskiya
Salla daukakace ga duk mai san daukaka, ita ce hanya kai tsaye ba tare da shamaki ba, domin ita ce ganawa da ubangiji. Kamar yadda ya zo a Kur'ani mai girma cewa “hakika ni ne ALLAH wanda ba wani ALLAH sai ni to ku bauta ...
Duk da cewa zancen annabi Sulaiman (a.s) ya na hikaya ne na daukakar matsayi da kuma yakini da Sulaiman ya ke da shi zuwa ga rahamar Allah marar karshe wanda ba za ka hada da sauran mutane ba, amma ba zaka hada da halin da imam Husain ...
Sabo kamar wani jiki ne mai wari da duk sa'dda aka nutse cikin yin sa to sai mutum ya rika jin warinsa ya ragu sakamakon ya zama jikinsa, domin zai daina jin warinsa daga karshe ya dulmuye cikinsa sosai. Kuma idan mutum ya yi azamar komawa daga ...
Ya kamata mu san cewa wannan aiki na wasa da azzakari haramun ne a mahangar muslunci sannan dukkanin mai aikata wannan aiki ya na cikin masu aikata manyan zunubai.[1] [2] Istimna”I {wasa da azzakari} kala-kala ne kamar misalin wasa da azzakari ...
Manzo (s.a.w) ya fada cikin mustahabbai da makaruhan jima’i cikin hadisi mai tsayi, ga Imam Ali (a.s) cewa: “ … ya Ali ka da ka tara da iyalinka cikin daren babbar salla domin idan Allah yai nufinku da samun da a wannan dare zai zamo mai yatsu ...