advanced Search
Dubawa
44862
Ranar Isar da Sako: 2012/03/15
Takaitacciyar Tambaya
Ta yaya Mutum zai iya samun ikon fassara Mafarki?
SWALI
Ta yaya Mutum zai iya samun ikon fassara Mafarki? Shin ko akwai Hadisi a kan haka?
Amsa a Dunkule

Mafarki wani al’amari ne dake faruwa ga dukkan mutane (a cikin barcinsu) a tsawon rayuwarsu. Sai dai har yanzu malamai ba su iya samun cikakkiyar saninsa ba da yadda yake faruwa.

Al’kar’ani mai girma ya bamu labarin Annabi Yusuf (a.s) game da mafarkinsa na gaskiya[1], kuma Allah ya hore masa fassara mafarki[2]. Kamar yadda ya fassara mafarkin abokan zamansa na kurkuku, da mafarkin Sarkin Misra, a wajen kurkuku ke nan dai fassarar mafarki, ko tawilin mafarki[3], a bisa irin kalmomin sunaye na Alkar’ani, shi al’amarine tabbatacce, na hakika, kuma wannan din wani ilimi ne wanda Allah ya sanar da wannan annabin, Annabi Daniyal yana daga cikin wadanda Allah ya ba su ilimin fassara mafarki[4]. Kuma hakika Kur’ani ya ambaci wasu shaidu na wasu Annabawan da Allah ya karfafa da gaskanta ingancin mafarkansu[5].

Game da rarraba ruwayoyi na nau’in mafarki, za mu ga kaso biyu na abubuwa da ake gani a cikin barci.

Wasu abubuwn da ake gani a cikin barci mafarkine na gaskiya, wasunsu kuma na karya ne[6]. ruwayoyi sun ambaci cewa; “Hakika mafarki na gaskiya wani yanki ne daga cikin yankin Saba’in na Annabaci”[7] shi irin wannan ilimin ba ana samunsa ne ta hanyar koyarwa da koyo ba, sai dai yana bukatar tazkiya da tsarkake rai, a saboda haka ne babu masu samun irin wannan baiwar sai yan mutane kadan kawai.

A cikin wasu littattafai na fassarara mafarki an ambaci wasu asasi da ka’idoji, sai dai ya wajaba mu lura da cewa wadannan asasin da ka’idojin, ba su ne komi da komi ba, kuma ba na gama gari ba ne, domin suna canzawa, a saboda bambaci su masu yin mafarkin, da wasu sharudda na daban. A saboda haka ba zai yiwu mu isa ga tabbatacciyar natija ba daga abubuwan da suka zo a cikin wadannan littattafaiba.

 


[1] Suratu yusuf, aya ta 4

[2] Suratu yusuf, aya ta 101

[3] Suratu yusuf, aya ta 101

[4] Littafin biharul anwar, wallafar allama majlisiy, juzu’I na 16, shafi na 371

[5] Suratus saffat, aya ta 105, da suratul fathi, aya ta 27.

[6] Littafin alkafiy, na kulayniy, juzu’I na 8, shafi na 91. bugun kamfanin, darul kutub al islamiyya.

[7] Littafin man la yahdhuruhul fakih, juzu’I na 2, shafi na 586

 

TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

  • menene hakikanin ma’anar salla?
    36439 Halayen Aiki 2012/07/25
    Salla daukakace ga duk mai san daukaka, ita ce hanya kai tsaye ba tare da shamaki ba, domin ita ce ganawa da ubangiji. Kamar yadda ya zo a Kur'ani mai girma cewa “hakika ni ne ALLAH wanda ba wani ALLAH sai ni to ku bauta ...
  • mece ce alakar jagorancin malami da jam'iyyu?
    7110 Tsare-tsare 2012/07/24
    Kungiyoyin siyasa, da ma'anar wasu jam'iyyu masu iri-iri akwai su a cikin kowace al'umma tun zamanin da. A yanzu ana ganin jam'iyyun siyasa a matsayin wani abu na tarayyar mutane da 'yancin zabe ne. bisa wannan asasin ne ya zama dole mu kalli wannan lamari a matsayin ...
  • Shin zai yiwu ai mana bayanin tafsirin suratu kausar?
    15332 Tafsiri 2017/06/17
    Suratu kausar sura ce da take da ayoyi guda uku, abin da ya fi shahara gun malamai shi ne an sauke ta a garin makka; sannan dalilin saukar ta shi ne yayewa manzon rahama (s.a.w) damuwar da yake ciki sakamakon mauta da gorin da wasu cikin kuraishawa ...
  • Ta yaya za a magance matsala, idan lamarin na hankali ya ci karon da na addini?
    14504 Sabon Kalam 2012/09/16
    Hankali shi ne hujjar Allah ta addini wacce ya ba wa mutum, hankali ke yi wa mutum jagora har ya kai shi ga samun cikakkiyar kamala, Shari`a hujja ce ta fili wacce take hana mutum gurbata da cutaya kuma ta kai shi ga samun cika da rabauta. ...
  • shin Imamul hujja a tsibirin bamuda yake zaune?
    15739 تاريخ بزرگان 2012/07/25
    Dalilin da ya sa wasu mutane suka yi ammanar cewa “Tsibirin Bamuda shi ne mazaunar Imamu Mahdi (a.s), gani suke Tsibirin Bamuda shi ne “Jazijrayul Khadra’a”. Bisa kaddara cewa Jaziratuk Khadra’a ita ce mazaunar Imamu Mahdi (a.s) shi ya sa suka ce Tsibirin Bamuda ya kunshi wadannan ...
  • Yaya aka samu sauyi a addinin Kiristanci, kuma da wane dalili ne ya samu karkacewa da jirkicewa
    12699 Sabon Kalam 2012/07/23
    Yayin da masu biyayya ga addinin Isa (a.s) suka haramata wa kawukansu wannan ni'ima ta samuwarsa a cikinsu, har ya samu hawa zuwa sama, sai manzanninsa da 'yan sakonsa suka ci gaba d aisar da sakonsa, kuma suka fuskanci wahalhalu masu yawa a kan hakan.
  • An lura da cewa Kur’ani mai girma shi ne mu’ujizar cika makin Manazannin Allah, to meye fuskokin gajiyarwar (kalu balen) da ke akwai a cikinsa?
    16211 Ilimin Kur'ani 2012/07/25
    An ambaci fuskokin gajiyarwar (kalu balen) da Kur’ani mai girma ya yi wadda zai yiwu na ambaci uku daga ciki: Ya gajiyar ta bangaren yare da bayani Ya gajiyar da fuskacin abin da ya kunsa Sannan kuma ya gajiyar ta ...
  • menene dalili a kan tabbatar shugabancin malami.
    18045 Hakoki da Hukuncin Shari'a 2012/07/26
    Akwai hanyoyi mabanbanta domin tabbatar da “shugabancin malami” sai dai a nan za mu isu da ambaton dalilai guda biyu na hankali da na ruwaya domin tabbatar da ita. Dalili na hankali: Hankali ya tabbatar da wajabcin samun mutumin da ke ...
  • Ta wace Hanya ake mangance maita da kanbun baka?
    40482 Halayen Aiki 2017/05/21
    Lalle Alkura'ani ma ya tabbatar da akwai maita, inda ya nuna wasu alamu da suke gaskata abin da tarihi ya tabbatar na daga cikin abin da Al’kur'anin ya zo da shi na daga al’umman da suka shude. Wasu malamai a wannan zamanin suna ganin wasu daga cikin ...
  • Menene hukunchi namijin da ba ya iya biyawa matarsa hakkokinta?
    13746 2019/06/16
    dawwamar rayuwar aure da karfafarta ya dogara da soyayya da kauna da fuskantar juna da girmama juna. Domin iyali su samu tsayuwa da dawwama Addini Muslunci ya sanya hakkoki ga kowanne dayansu ya kuma ayyana musu wajibai a kansu, duk sa”ilin da aka ce akwai hakkoki to ...

Mafi Dubawa