advanced Search
Dubawa
38342
Ranar Isar da Sako: 2017/05/22
Takaitacciyar Tambaya
Shin zai yiyu a sami alaKa tsakanin Mutum da Aljani?.
SWALI
Shin zai yiyu Dan’adam ya yi akaKa da aljani? Idan har zai yiyu, ya hukuncin yin haka yake?
Amsa a Dunkule
Kur'ani mai girma ya tabbatar da samuwar aljani kuma ga wasu daga cikin bayanai kan aljani.
1-            Aljani halittace da aka yi shi da wuta saBanin mutum shi da kasa aka halicce shi.[1]
2-            Yana da ilimi da idraki da tantance Karya daga gaskiya, yana iya yin magana kuma yana kafa dalili.[2]
3-            An wajabta masa ayyuka (na ibada da dss) da kuma nauyaye nauyaye.[3]
4-            Wasu daga cikin su muminai ne salihai wasu kuma kafirai.[4]
5-            Za a tashe su ranar alkiyama kuwa za a yi musu hisabi.[5]
6-            Suna iya keta sararin samaniya su sato ji amma daga baya an hana su.[6]
7-             Suna kulla alaka da wasu daga cikin mutane kuma suna yin amfani da masaniyar da suke da ita na wasu Boyayyaun sirrika su halakar da mutane.[7]
8-            A cikin su akwai waDanda suke da karfin da iko na gaske kamar yadda ake samu a cikin mutane.[8]
9-             Suna da ikon yin wasu ayyuka da mutane ke bukatuwa zuwa gare su[9].
10-          Su aka fara halitta a doron kasa kafin ahalicci mutane[10].
11-          A cikin Kissar Annabi sulaiman (as) lokacin da Ifritu daga cikin aljanu ya yi da’awar cewa zai iya kawo gadon BilKisu wajen Annabi Sulaiman (as) kafin ya tashi daga mazauninsa[11], Annabi Sulaiman (as) bai Karyata shi ba duk da cewa wannan maganar ba ta zo a cikin Kur'ani ba cewa ya kawo gadon ba[12]
Daga cikin abin da aka amabata a cikin yoyiyn da muka kawo zamu fahimci cewa aljanni ba halitta ce irin ta tatsuniya da labara ba, shi halitta ne samamme a haKiKa, mai jiki wanda za a iya yin alaKa da shi, kuma wasu daga cikin mutane sun yi alaKa da shi, duk da cewa a zamanin da an fadi wasu nau’o’i na alaka daban daban tsakanin mutane da aljani, amma mu zamu takaitu da irin wacce muka samu a cikin Kur'ani da hadisi, da ita zamu isu don wannan kawai muka yarda da shi.
A nan za mu yi nuni zuwa ga yanayin alaKar da muka samu a cikin Kur'ani da ruwayoyi da kuma maganganun da aka naKalto daga wasu maKiya:
A.            Neman tsarin Allah daga aljanai; ya zo a Kur'ani mai girma cewa: {haKiKa wasu mazaje daga mutane sun kasance suna neman tsari wajen wasu mazaje daga aljanu sai suka kara jefa su cikin bala’i da “wahala”}[13].
Al’adar larabawa ta kasance duk lokacin da suka shiga daji mai ban tsoro (misali mai duhuwa) suna neman tsari daga aljanun wannan kwazazzabon, kuma musulunci bai hana yin haka ba kuma ya yi umarni da a nemi tsari daga shaiDanun mutane da na aljan[14].
B.             Tasarrufi da aljani; yin tasarrufi da aljani da yin amfani da su wajen yin hidima duk da cewa abu ne mai yiyuwa, sai dai malamai sun yi bahasi kan cewa shi ya halatta ko kuwa? Gwargwadon abin da suka yarda da shi, shi ne lalle ne kar wannan aikin ya zama ta hanyar da shari’a ta haramta, ko kuma ya zama sanadin cutuwar aljanu. Kuma lalle ne ya zama aikin da suke yi ba wanda shari’a ta haramta ba ne. kuma lalle yin aikin da shari’a ba ta yarda da shi ba ya haramta daidai ne da wasiDa ko babu wasiDa.[15]
An tambayi Marja’I Mai girma Sayyid Ali (as) Khamna’i kan hukuncin zuwa wajen mutanen da ke tasarrufi da rauhanai da aljanu wajen yi wa mutane magani tare da la’akari da cewa bisa  yaKini su aikin alkhairi kawai suke yi, sai ya bada amsa da cewa: wannan aikin ba shi da mushkila a kan kansa da sharaDin cewa ya zama yana yin aiki ta hanyar da shari’a ta halatta[16].
Domin samun Karin bayani a komawa jigogi masu zuwa:-
1.             Abin da sheDan a aljani suke iya yi, tambaya ta 883.
2.             SheDan mala’ika ne ko aljani? Tambaya ta 857.
3.             Littafin aljani da sheDan na Ali Ridha, Tehrani. wanda aka yi tahKiKinsa a mahanga ta Kur’ni da ruwaya da hankali da ilimin rijalu (mazajen hadisi). 
 

[1] Surar rahaman aya 15.
[2] Ayoyi mabanbanta a cikin surar Jinni.
[3] Ayoyi mabanbanta a cikin surar Jinni da Rahaman.
[4] Ayoyi mabanbanta a cikin surar Jinni da Rahaman.
[5] Adreshin da ya gabata 15.
[6] Adreshin da ya gabata 9.
[7] Adreshin da ya gabata 6.
[8] Surar Namli aya 39.
[9] Surar Saba’i aya ta 12 da 13.
[10] Surar Hijiri aya ta 27.
[11] Surar Tururuwa aya ta 30 – 40.
[12] Jawadi Amuli Abdullah a cikin tafsirul maudhu’I j1 shafi 119.
[13] Surar Jinni aya ta 6.
[14] Biharul Anwar j 92 shafi 148 (almahasin) Manzo (saw) ya ce: “Idan masihirtan aljanu su ka motsa, ku kare sharrinsu da kiran salla”.
[15] Mihajus Salihin na sayyid khu’I j 2 shafi na 8.
[16] Taudhihul  masa’il (mai hashiya na Imam khomaini) j 2 shafi 980, 1232.
TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

  • menene hakikanin ma’anar salla?
    36439 Halayen Aiki 2012/07/25
    Salla daukakace ga duk mai san daukaka, ita ce hanya kai tsaye ba tare da shamaki ba, domin ita ce ganawa da ubangiji. Kamar yadda ya zo a Kur'ani mai girma cewa “hakika ni ne ALLAH wanda ba wani ALLAH sai ni to ku bauta ...
  • mece ce alakar jagorancin malami da jam'iyyu?
    7110 Tsare-tsare 2012/07/24
    Kungiyoyin siyasa, da ma'anar wasu jam'iyyu masu iri-iri akwai su a cikin kowace al'umma tun zamanin da. A yanzu ana ganin jam'iyyun siyasa a matsayin wani abu na tarayyar mutane da 'yancin zabe ne. bisa wannan asasin ne ya zama dole mu kalli wannan lamari a matsayin ...
  • Shin zai yiwu ai mana bayanin tafsirin suratu kausar?
    15332 Tafsiri 2017/06/17
    Suratu kausar sura ce da take da ayoyi guda uku, abin da ya fi shahara gun malamai shi ne an sauke ta a garin makka; sannan dalilin saukar ta shi ne yayewa manzon rahama (s.a.w) damuwar da yake ciki sakamakon mauta da gorin da wasu cikin kuraishawa ...
  • Ta yaya za a magance matsala, idan lamarin na hankali ya ci karon da na addini?
    14504 Sabon Kalam 2012/09/16
    Hankali shi ne hujjar Allah ta addini wacce ya ba wa mutum, hankali ke yi wa mutum jagora har ya kai shi ga samun cikakkiyar kamala, Shari`a hujja ce ta fili wacce take hana mutum gurbata da cutaya kuma ta kai shi ga samun cika da rabauta. ...
  • shin Imamul hujja a tsibirin bamuda yake zaune?
    15739 تاريخ بزرگان 2012/07/25
    Dalilin da ya sa wasu mutane suka yi ammanar cewa “Tsibirin Bamuda shi ne mazaunar Imamu Mahdi (a.s), gani suke Tsibirin Bamuda shi ne “Jazijrayul Khadra’a”. Bisa kaddara cewa Jaziratuk Khadra’a ita ce mazaunar Imamu Mahdi (a.s) shi ya sa suka ce Tsibirin Bamuda ya kunshi wadannan ...
  • Yaya aka samu sauyi a addinin Kiristanci, kuma da wane dalili ne ya samu karkacewa da jirkicewa
    12699 Sabon Kalam 2012/07/23
    Yayin da masu biyayya ga addinin Isa (a.s) suka haramata wa kawukansu wannan ni'ima ta samuwarsa a cikinsu, har ya samu hawa zuwa sama, sai manzanninsa da 'yan sakonsa suka ci gaba d aisar da sakonsa, kuma suka fuskanci wahalhalu masu yawa a kan hakan.
  • An lura da cewa Kur’ani mai girma shi ne mu’ujizar cika makin Manazannin Allah, to meye fuskokin gajiyarwar (kalu balen) da ke akwai a cikinsa?
    16211 Ilimin Kur'ani 2012/07/25
    An ambaci fuskokin gajiyarwar (kalu balen) da Kur’ani mai girma ya yi wadda zai yiwu na ambaci uku daga ciki: Ya gajiyar ta bangaren yare da bayani Ya gajiyar da fuskacin abin da ya kunsa Sannan kuma ya gajiyar ta ...
  • menene dalili a kan tabbatar shugabancin malami.
    18045 Hakoki da Hukuncin Shari'a 2012/07/26
    Akwai hanyoyi mabanbanta domin tabbatar da “shugabancin malami” sai dai a nan za mu isu da ambaton dalilai guda biyu na hankali da na ruwaya domin tabbatar da ita. Dalili na hankali: Hankali ya tabbatar da wajabcin samun mutumin da ke ...
  • Ta wace Hanya ake mangance maita da kanbun baka?
    40482 Halayen Aiki 2017/05/21
    Lalle Alkura'ani ma ya tabbatar da akwai maita, inda ya nuna wasu alamu da suke gaskata abin da tarihi ya tabbatar na daga cikin abin da Al’kur'anin ya zo da shi na daga al’umman da suka shude. Wasu malamai a wannan zamanin suna ganin wasu daga cikin ...
  • Menene hukunchi namijin da ba ya iya biyawa matarsa hakkokinta?
    13746 2019/06/16
    dawwamar rayuwar aure da karfafarta ya dogara da soyayya da kauna da fuskantar juna da girmama juna. Domin iyali su samu tsayuwa da dawwama Addini Muslunci ya sanya hakkoki ga kowanne dayansu ya kuma ayyana musu wajibai a kansu, duk sa”ilin da aka ce akwai hakkoki to ...

Mafi Dubawa