advanced Search
Dubawa
4273
Ranar Isar da Sako: 2019/05/15
Takaitacciyar Tambaya
Shin Ammar Dan Yasir ya temaka wa Imam Ali (a.s) kan lamarin da ya faru a SaKifa ko kuwa?
SWALI
Ina yin sallama a gare su, Dangane da abin da ya wakana a SaKifa, shin Ammar Dan Yasir ya temaki Ali (a.s) ko kuwa?
Amsa a Dunkule
Mutane da dama sun tafi kan cewa Imam Ali shi ne shugabansu, amma yanayin yanda suke yi masa biyayya kuma suka sallam masa ya banbanta, babu tantama tun a farko Ammar ya kasance matemaki kuma mabiyu wanda ya sallamawa imama Ali (a.s) duk da cewa ta yiyu wani abu ya Darsu a cikin zuciyarsu cewa me ya sa Imam ya zaBi yin shiru, me ya sa be zare takobinsa ba, saboda me........? dss.
«عَلِیُّ بْنُ الْحَکَمِ، عَنْ سَیْفِ بْنِ عَمِیرَةَ عَنْ أَبِی بَکْرٍ الْحَضْرَمِیِّ، قَالَ: قَالَ أَبُو جَعْفَرٍ (ع) ارْتَدَّ النَّاسُ إِلَّا ثَلَاثَةَ نَفَرٍ سَلْمَانُ وَ أَبُو ذَرٍّ وَ الْمِقْدَادُ. قَالَ قُلْتُ فَعَمَّارٌ قَالَ قَدْ کَانَ جَاضَ جِیضَةً، ثُمَّ رَجَعَ، ثُمَّ قَالَ إِنْ أَرَدْتَ الَّذِی لَمْ یَشُکَّ وَ لَمْ یَدْخُلْهُ شَیْ‏ءٌ فَالْمِقْدَادُ، فَأَمَّا سَلْمَانُ فَإِنَّهُ عُرِضَ فِی قَلْبِهِ عَارِضٌ أَنَّ عِنْدَ أَمِیرِ الْمُؤْمِنِینَ (ع) اسْمَ اللَّهِ الْأَعْظَمَ لَوْ تَکَلَّمَ بِهِ لَأَخَذَتْهُمُ الْأَرْضُ وَ هُوَ هَکَذَا فَلُبِّبَ وَ وُجِئَتْ، عُنُقُهُ حَتَّى تُرِکَتْ کَالسِّلْقَةِ، فَمَرَّ بِهِ أَمِیرُ الْمُؤْمِنِینَ (ع) فَقَالَ لَهُ یَا أَبَا عَبْدِ اللَّهِ هَذَا مِنْ ذَاکَ بَایِعْ! فَبَایَعَ وَ أَمَّا أَبُو ذَرٍّ فَأَمَرَهُ أَمِیرُ الْمُؤْمِنِینَ (ع) بِالسُّکُوتِ وَ لَمْ یَکُنْ یَأْخُذُهُ فِی اللَّهِ لَوْمَةَ لَائِمٍ فَأَبَى إِلَّا أَنْ یَتَکَلَّمَ»؛
“An karBo daga Ali Dan Hakam daga Saifu Dan Umairu daga Baban Bikri bahadhrame, ya ce: Abu Ja”afar  (a.s) ya ce dukkanin mutane sun yi ridda bayan Manzon Allah (s.a.w) in banda mutum uku, Salman da Abuzarri da MiKdad, ya ce sai na ce Ammar fa? sai ya ce: ya kasance ya raurawa sanna ya dawo, idan kana nufin wanda be yi shakku ba wanda shi ne kuma wani abu bai raurawar da shi ba to MiKdad ne, amma Salman ya kasance yana ganin cewa Imam Ali na da sunan Allah mafi girma wanda da ina ma zai roki Allah da shi, da kasa ta kamasu sun halaka baki Daya, kuma haka ne. amma Abuzarri haKiKa Imam Ali ya umarce shi da ya yi shiru (saboda tausaya wa a gare shi ba bisa umarni ba), domin ya kasance ba ya jin tsoron zargin mai zargi kal lamarin Ubangiji , sai ya Ki ya yi shiru ya ci gaba da magana”. [1]
La’akari da yanayin da musulunci ya ke ciki a farkon kira, na kasancewar sa sabon kafawa kuma sabon addini, wamda ke kewaye da haDurra masu yawa, na daga abokan gaba na cikin gida da ma na waje, waDannan dalilai zasu iya zama sirrin da ya sa Ahlulbaiti suka yi wa wasu daga  cikin sarakuna shiru, kuma wannan ne ma yasan Salman da Ammar suka yi aiki tare da hukamomi abin da ya fi wannan shi ne hidimar da Imam Ali (a.s) ya gabatar da temaka wa halifofi zai kusanto da wannan mahangar.  Da wani yaren bisa la’akari da yanayin da musulunci ke ciki da kuma kokarin kare wanzuwarsa da bada gudun mawa wajen cigabantar da shi, ba abin da zai hana Imam ma’asumi ya yi aiki tare da halifofi,[2] kumar yanda Salman da Ammar ma sun karBi matsayin gomnoni a garin Mada’in da Kufa da izinin Imam Ali (a.s).[3]
 
 

[1]. Kashshi, Muhammad  bini Umar, ikhtiyari ma’arifatul rijal, shafi 11, muassasr nashri danashgah, mashhad, bugu na Daya shekara ta 1409. Shekh mufid, al-ikhtisas, wanda aka yiwa tahKiKi aka gyara, gaffari, Ali akbar, muharrami zirnadi, Mahmud, Mahmud, shafi na 10, mu’atamarul alami lil’alfiyati shekh mufid, Kum, buga na daya, 1413.     
[2]. Saboda haka ne ma Imam Ali (a.s) yake cewa “zan sallama matuKar al’ummar musulmai zasu sallama kuma ya zama ba wanda ake zalunta sai ni kaDai” nahjul balaga, tarjamar Dashti, Muhammad  khuDba, ta 74, shafi na 122 -123; da ibni abinl hadidi j 6 sh 166; subhi salih, 102.
[3]  La’akari da yanda waDannan manyan suka sallama wa Imam Ali (a.s), yana da marukar wahalar gaske a ce sun karBi waDannan manyan ayyuka na hukuma ba tare da izinin Imam Ali (a.s) ba.
TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

  • menene hakikanin ma’anar salla?
    36439 Halayen Aiki 2012/07/25
    Salla daukakace ga duk mai san daukaka, ita ce hanya kai tsaye ba tare da shamaki ba, domin ita ce ganawa da ubangiji. Kamar yadda ya zo a Kur'ani mai girma cewa “hakika ni ne ALLAH wanda ba wani ALLAH sai ni to ku bauta ...
  • mece ce alakar jagorancin malami da jam'iyyu?
    7110 Tsare-tsare 2012/07/24
    Kungiyoyin siyasa, da ma'anar wasu jam'iyyu masu iri-iri akwai su a cikin kowace al'umma tun zamanin da. A yanzu ana ganin jam'iyyun siyasa a matsayin wani abu na tarayyar mutane da 'yancin zabe ne. bisa wannan asasin ne ya zama dole mu kalli wannan lamari a matsayin ...
  • Shin zai yiwu ai mana bayanin tafsirin suratu kausar?
    15332 Tafsiri 2017/06/17
    Suratu kausar sura ce da take da ayoyi guda uku, abin da ya fi shahara gun malamai shi ne an sauke ta a garin makka; sannan dalilin saukar ta shi ne yayewa manzon rahama (s.a.w) damuwar da yake ciki sakamakon mauta da gorin da wasu cikin kuraishawa ...
  • Ta yaya za a magance matsala, idan lamarin na hankali ya ci karon da na addini?
    14504 Sabon Kalam 2012/09/16
    Hankali shi ne hujjar Allah ta addini wacce ya ba wa mutum, hankali ke yi wa mutum jagora har ya kai shi ga samun cikakkiyar kamala, Shari`a hujja ce ta fili wacce take hana mutum gurbata da cutaya kuma ta kai shi ga samun cika da rabauta. ...
  • shin Imamul hujja a tsibirin bamuda yake zaune?
    15739 تاريخ بزرگان 2012/07/25
    Dalilin da ya sa wasu mutane suka yi ammanar cewa “Tsibirin Bamuda shi ne mazaunar Imamu Mahdi (a.s), gani suke Tsibirin Bamuda shi ne “Jazijrayul Khadra’a”. Bisa kaddara cewa Jaziratuk Khadra’a ita ce mazaunar Imamu Mahdi (a.s) shi ya sa suka ce Tsibirin Bamuda ya kunshi wadannan ...
  • Yaya aka samu sauyi a addinin Kiristanci, kuma da wane dalili ne ya samu karkacewa da jirkicewa
    12699 Sabon Kalam 2012/07/23
    Yayin da masu biyayya ga addinin Isa (a.s) suka haramata wa kawukansu wannan ni'ima ta samuwarsa a cikinsu, har ya samu hawa zuwa sama, sai manzanninsa da 'yan sakonsa suka ci gaba d aisar da sakonsa, kuma suka fuskanci wahalhalu masu yawa a kan hakan.
  • An lura da cewa Kur’ani mai girma shi ne mu’ujizar cika makin Manazannin Allah, to meye fuskokin gajiyarwar (kalu balen) da ke akwai a cikinsa?
    16211 Ilimin Kur'ani 2012/07/25
    An ambaci fuskokin gajiyarwar (kalu balen) da Kur’ani mai girma ya yi wadda zai yiwu na ambaci uku daga ciki: Ya gajiyar ta bangaren yare da bayani Ya gajiyar da fuskacin abin da ya kunsa Sannan kuma ya gajiyar ta ...
  • menene dalili a kan tabbatar shugabancin malami.
    18045 Hakoki da Hukuncin Shari'a 2012/07/26
    Akwai hanyoyi mabanbanta domin tabbatar da “shugabancin malami” sai dai a nan za mu isu da ambaton dalilai guda biyu na hankali da na ruwaya domin tabbatar da ita. Dalili na hankali: Hankali ya tabbatar da wajabcin samun mutumin da ke ...
  • Ta wace Hanya ake mangance maita da kanbun baka?
    40482 Halayen Aiki 2017/05/21
    Lalle Alkura'ani ma ya tabbatar da akwai maita, inda ya nuna wasu alamu da suke gaskata abin da tarihi ya tabbatar na daga cikin abin da Al’kur'anin ya zo da shi na daga al’umman da suka shude. Wasu malamai a wannan zamanin suna ganin wasu daga cikin ...
  • Menene hukunchi namijin da ba ya iya biyawa matarsa hakkokinta?
    13746 2019/06/16
    dawwamar rayuwar aure da karfafarta ya dogara da soyayya da kauna da fuskantar juna da girmama juna. Domin iyali su samu tsayuwa da dawwama Addini Muslunci ya sanya hakkoki ga kowanne dayansu ya kuma ayyana musu wajibai a kansu, duk sa”ilin da aka ce akwai hakkoki to ...

Mafi Dubawa