advanced Search
Dubawa
82066
Ranar Isar da Sako: 2019/06/16
Takaitacciyar Tambaya
Illolin wasa da azzakari, manyan zunubai, wankan janaba, dalilan haramci
SWALI
menene hukuncin wanda ke yin wasa da azzakarinsa har ya kai gafitar da maniyyi?
Amsa a Dunkule
Ya kamata mu san cewa wannan aiki na wasa da azzakari haramun ne a mahangar muslunci sannan dukkanin mai aikata wannan aiki ya na cikin masu aikata manyan zunubai.[1]  [2]
Istimna”I {wasa da azzakari} kala-kala ne kamar misalin wasa da azzakari da hannu da kuma misalin sauraren muryar macen da ba muharrama ba, ko kuma yin musayen kalaman soyayya, da yin tunanin abubuwada masu matso sha”awa.
Dukkanin wanda ya yi amfani da daya daga cikin wadannan abubuwa da muka ambata suka kai shi ga fitar da maniyyi to wannan aikin nasa sunansa istimna”I wanda yake haram ne.[3]
Wajibi ne wanda yake aikata wannan mummunar dabi”a ya tuba ya kuma yi wankan janaba don cika sharuddan ibada, tabbas dukkanin wanda ya daura damarar kuma ya yi aniyar tuba da barin wannan mummunan aiki ya kuma nemi taimakon ubangiji a kai to ubangiji zai taimaka masa.[4]
Ya zo a Cikin hadisai masu tarin yawa cewa an yi hani kan wannan mummunar dabi”a ta istimna”i.
Manzon Allah {s.a.w} yana cewa: dukkanin wanda yake auren tafin hannunsa {wasa da azzakari} ya nesanta da ga rahamar ubangiji.
Abu basir yana cewa na ji daga imam sadik {as} yana cewa: ubangiji ba zai Magana da nau”o’in mutane uku ba kuma ba zai kale su ba, kuma ba zasu tsarkaka daga zunubai ba kuma azaba mai radadi na jiransu. Daya daga cikin wadanna gungun sune wadanda suka kasance suna aurar tafin hannunsu wato suna (wasa da zakarinsu har sai maniyyi ya fita).
An tambayi imam sadik kan mummunar al’ada ta boye (wasa da zakari), yayin da yake ba da amsa sai ya ce: babban zunubi ne kuma wanda Allah madaukaki yayi hani da shi a cikin littafinsa mai tsarki kuma wanda yake yin wannan aikin tamkar wanda ya auri kansa ne kuma idan har na san wani yana aikata haka ba zan ci abinci tare da shi ba. Sai mai tambaya ya ce: ya dan manzon Allah (saw) yi mana bayanin hanin Allah a cikin littafinsa: sai ya ce wanda yake neman biyan bukatarsa {ba ta hanyar da Allah ya halatta ba} to azzalumi ne shi.
Bari mu kawo muku wasu wasu shashi ne daga ruwayoyin da ke yin nuna kan tsananin kin Allah ga wannnan aiki da kuma haramcinsa.[5]
Daya daga cikn dalailan da suka sa musulumci ya haramta wannan aiki shi ne, irin cututtuka msau yawa da yake jawo wa jika da ruhi da hankali kuma a yau ci gaban ilimi ya gano wasu daga cikinsu. Kuma mai yiyuwa nan gaba a karo gano wasu illolin na daban.[6] A yau an gano illolin da wasa da zakari ke haifarwa wadannan zamu iya kasa su zuwa kaso biyu:
 
Na daya: cututuka na ruhi.
  1. Wannan zunbuni na nesanta mutum daga Allah ta yadda a ranar lahira Allah ta’ala ko kallon masu wannan laifi ba zai yi ba kuma ba zai yi Magana da su ba kuma yana hana su samun wasu abubuwa mihimmai kamar tsarkakakken ruhi da nisantar abubuwan da aka haramta dss.
  2. A sakamakon bin tauyayayyar hanyar biyna bukata wacce ba ta dabi’a ba, bayan da mai wannan dabi’a ya yi aure mafi yawa ba sa iya zama da matansu kamar yadda ya kamata zaka same shi rarrauna wajen biyna bukatar matarsa ta kwanciya, kari a kan matsaloli na zamantakewar yau na gobe, daga karshe hakan ya kai ga tarwatsewar rayuwarsu ta aure.
  3. Mutuwar jiki da rashin damuwa da abubuwa mihimmai na rayuwa, yawan damuwa da kunci da ma wasu illoli da suka shafi ruhi.
  4. Yana jawo dakushewar tunani da daidaitar tunani da raunin harda da raunanan himma.
  5. Yawaita sanyin jiki da rudewa dss.
  6. Saurin gajiya da raunanar jijiyoyin da ke karfafa ruhi.
  7. Saurin jin gajiya daga karamar wahala da daukar zafi a mafi karancin taho mu gama da wasu.
Na buyu: cututtuka na jiki:
  1. Wannan ya jarrabtu da wannan dabi’ar yana fama da matsaloli na ruhi da jiki kuma a sannu a sannu sai ya wayi gari rarrauna, wanda ba ya iya komai, wanda bai san ciwon kansa ba, mai debe tsammani. da ga karshe sai ya zama wanda hankalinsa ya tabu kuma ya rika yi wa wasu mummunan kallo.
  2. Yawaita motsa al’aurarsa da wuce iyaka da bawa gabbai saduwa aikin tukuru na jawo saurin girma da tsufa.
  3. Yawan maimata wannan aiki na jwo gaba dayan jiki  ya yi rauni daga karshe nan da nan sai ya tsofe.
  4. Saboda yawan gudanar jinni a cikin gabbai masu haihuwa, kwakwakwarsa da sauran gabbai na samun rauni wajen iya gudanar da jinni kamar yadda ya kamata.
  5. Yawan tayar da jijiyoyi da rashin gamsuwa a lokaci mai tsawo na sa jijiyoyi su yi rauni kuma hakan na taba ruhin mutum.
  6. Raunana gani da rashin jin dandano da raunin kashi da ciwon gabbai.
  7. Kamuwa da cutar karancin jini, musamman ma sakamakon yawaita motsa zakari a koda yaushe.  
  8. Lalacewar ma’ajiyar maniyyi.
  9. Lalacewar babgaren karkashin ma’ajira maniyyi da kuma gabansa.
  10. Lalacewa gabban haihuwa kamar rashin iya rike maniyyi da kuma rashi iya rike fitsari.
Abin lura a nan shi ne duk da cewa an yi bayanin illolin da istim’na’I yake haifarwa, sai dai ba za mu iya cewa dalilin da ya sa aka haramta shi su ne wadanda muka ambata a nan kadai ba.[7] Ballantana ma zai iya yiyuwa suna da wasu illolin na jiki da na ruhi na daban wadanda har yanzu ba mu san su ba, don haka muna da tabbacin cewa hukunce-hukuncen da suke daga Allah ta’ala baki dayansu sun doru ne kan mas’laha da barna.                         
 
 

[1] An sanya wannan laifi daga cikin jerin zina kamar yadda ya zo a ruwaya cikin wasa;ilu shi’a j20 shafi 352.
[2] A dakko daga tambaya ta 326.  
[3] Mujma”ulrasa”il muhashsha shafi 34 da manasik na imam khomaini shafi 163 da shafi 334.
[4] Don samun bayani sosai kan hanyoyin barin isimna’I a koma tambaya ta 2294.
[5] An ciro daga tambaya ta 1262.  
[6] An ciro daga tambaya ta 1575.
[7] An ciro daga tanbaya ta 1744.  
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

Mafi Dubawa