advanced Search
Dubawa
5965
Ranar Isar da Sako: 2014/05/24
Takaitacciyar Tambaya
Menene Hukuncin musulmin da ya kashe kafirin da ba bazimme ba?
SWALI
Idan musulmi ya kashe kafirin da ba bazaimme ba yaya hukuncin yake?
Amsa a Dunkule
Hukuncin musulumci kan kisa idan na gangan ne kisasi za a yi (Kisasi shi ne kashe wanda ya yi kisan kai) idan kuma ba na gangan ba ne diyya za abiya. Amma kafin a yiwa wanda ya yi kisan kai Kisasi akwai sharaDai da ya zama idan har ko da Daya daga cikin su bai tabbata ba, ba za a zartar da hukuncin Kisasi a kansa ba. don haka la’akari da cewa Daya daga cikin sharaDan Kisasi a mahangar fiKihu da doka shi ne daidaito tsakanin wanda aka kashe da wanda ya yi kisa. Daukaki malaman Shi'a kai tsaye suna cewa; ba a kashe musulmi idan ya kashe kafiri, sai dai in musulmin da ya kashe kafiri bazimme yin kisan ya zame masa la’ada (wato ya saba kashe bazimme ba sau daya ba ba sau biyu ba). A wannan yanayin bisa ra’ayi mafi rinjaye ya halarta a kashe wannan musulmin. Amma malamai sun sassaBa kan dalilin kashe musulmin, wasu sun tafi kan cewa saboda ya yi kisan kai ne wasu kuma suna ganin saboda yana yaDa barna a bayan kasa ne.    
Amma idan musulmin da ya yi kisan ya zama kashe bazimme bai zame masa al’ada ba, to ba za a yi masa Kisasi ba bisa mashhuriyar magana, idan msulmi ya kashe bazimme za a tilasta masa biyan diyya kuma za a yi masa horo (wato ta’aziri da larabci), amma da a ce kafirin da ya kashe ba bazimme ba ne Karin a kan cewa babu Kisasi a kansa, haka ma ba za ya biya diyya ba.
An yi amfani da ra’ayi mashhuri kan hukuncin diyyar kafiri bazimme a yayin da aka yi amfani ra’ayin da ba mashhuri ba kan diyya kafirin da ba bazimme ba, don haka ya zo a doka cewa: idan musulmi ya yi wa kafiri ko wane iri ne rauni bazimme ne ko ba bazimme ba, kai hatta wadanda suke na amana da na alkawari, to ba za a yi masa kisasi ba, amma zai biya diyya kuma za a yi masa ta’aziri idan ya kashe ko wane irin kafiri hatta waDanda ba na amana da waDanda ba na alkawani ba.       
Amsa Dalla-dalla
Raunin da Dab’adam ke yi wa waninsa ya kan iya zama kisan kai ko cire wata gaBa ko kuma raunanata. Kuma raunin yin kisa dss, sun kasu kaso uku; da gangan, ko wamda ya yi kama da gangan ko kuma na kuskure.
Ya zo a cikin shari’a mai tsarki cewa {kuma mun rubuta musu a cikinta (Attaura) cewa; lalle rai a maimakon rai, ido a maimakon ido, hanci da hanci, kunne da kunne, haKori da haKori, raunika kuma hukuncinsu Kisasi ne, wanda kuma ya yi afwa ya yafe, ya zama kaffara a gare shi (shi ya fi dace wa kuma an so ya yi haka), duk wadanda ba su yi hukunci da abin da Allah ya saukar ba to waDannan su ne azzalumai}[1].  
Idan zubar da jina ya zama ba da gangan ba[2], wanda kisa daya Daga cikin zubar da jini ne, hukuncin sa ya zo a cikin aya {Bai halatta ga mumini ya kashe mumini ba in ba bisa kuskure ba, duk wanda ya kashe mumini sai ya ’yanta wuyaye (baiwa) mumina ya kuma biya diyyar da za a bawa ahalinsa (shi wanda aka kashe din) sai dai in sun yafe}[3].
Don haka magana kan cewa idan musulmi ya yiwa kafiri bazimme ko wanda ma ba bazimme ba rauni ko ya kashe shi, hukuncinsa na komawa ga wannan ayar ne ko kuwa? Ma’ana wanda ya yi kisan kai za a yi masa hukunci da Kisasi ko kuma zai bada diyya? Donin samun Karin bayani kan kashe-kashen kafiri a mahangar fiKihu da kalam, sai a koma wa jigon kashe-kashen kafirai tambaya mai namba 27147.
Kuhunce-Hukuncen Kashe Kafiri A Hannun Musulmi
La’akari da cewa mahangar fiKihu da ta doka, Daya daga cikin sharaDan Kisasi[4] shi ne daidaito tsakanin wanda ya yi kisan kai da wanda aka kashe, malaman Shi'a kai tsaye sun tafi kan cewa ba a kashe musulmi da kafiri[5] in danda musulmin da ya kashe kafirin bazimme ya zame masa al’ada ba[6] a irin wannan yanayin gina bisa mash’hurin ra’ayi, ya halatta a kashe wannan musulmin, duk da cewa hukuncin kisan da ya hau kansa saboda ya yi kisan kai ne wato kisasi ne ko kuma saboda ya zama mai yaDa Barna a bayan kasa ne ko kuma ta saboda ya na muharaba (fito-na-fito da Allah)[7], malamai sun saBa kan wannan hukuncin[8].
Amma idan kashe kafiri ba zimme bai zame wa musulmin da ya yi kisan al’ada ba, ba za a yi masa kisasi ba, za a tilasta masa biyan diyya kuma a yi masa[9] horo[10] amma idan ya zama kafirin da aka kashe ba bazimme ba ne ko da kuma kafirin “amana”[11] ne ko na “alkawari”[12] bisa ra’ayi mashhuri, bayan cewa ba za a yi masa Kisasi ba haka ma kuma ba zai biya diyya ba[13].
An yi amfani da ra’ayi mashhuri kan hukuncin diyyar kafiri bazimme a yayin da aka yi amfani ra’ayin da ba mashhuri ba kan diyya kafirin da ba bazimme ba, don haka ya zo a doka cewa: idan musulmi ya yi wa kafiri ko wane iri ne rauni bazimme ne ko ba bazimme ba na’amana da na alkawari kai hatta wadanda suke na amana da na alkawari, to ba za a yi masa kisasi ba, amma zai biy diyya kuma za a yi masa ta’aziri idan ya kashe ko wane irin kafiri hatta waDanda ba na amana da waDanda ba na alkawani ba.

[1] {Kuma muka rubuta musu a cikinta wato (Attaura) cewa; lalle rai a maimakon rai, ido a maimakon ido, hanci da hanci kunne da kunne haKori da haKori, raunika kuma hukuncinsu Kisasi ne, wanda kuma ya yi afwa ya yafe, ya zama kaffara a gare shi (shi ya fi zama ya dace kuma an so ya yi haka), duk wanda bai yi hukunci da abin da Allah ya saukar ba to waDannan su ne azzalumai”
[2] kuskure tsantsa da kuma kisan da ya yi kama da na gangan.
[3]  “Bai halatta ga mumini ya kashe mumini ba in ba bisa kuskure ba, duk wanda ya kashe mumini sai ya ’yanta wuyaye (baiwa) mumina ya kuma biya diyyar da za a bawa ahalinsa ( shi wanda aka kace) sai dai in sun yafe”.
[4] Sharadan kisasi su ne: 1. Daidaito a cikin ‘yanci da ne shi ko bawa. 2. Daidaito a cikin addini. 3. Rashi uba, (wanda za a yiwa kisasi ya zama dan shega) 4. Hankali 5. Balaga 6. Mai tsararren jinni (wanda aka kashe ya zama jininsa na da kima da daraja). Khomaini Musawi  sayyin Ruhulllah, Tahrirul wasila j 2 shafi 519 – 523 mu’assasat madbu’at darul ilmi Kum, bugu na farko.
[5] Ya wuca iyakacin kafiri kawai ya hada da wanda  ya yi ridda na asali da bazimme da na yaki da na alkawari da na amana  da ma wnada ba na alkawari ba.
[6] Hukumar Musulunci ita ce ke yin yarjejeniya a da kafiri daga nan ake kiran wannan kafirin (Bazimme), bisa wannan hukumar musulunic zata rika karbar kudi a hannunsa da sunan jiziya tana kare shi da iyalinsa da dukiyarsa kamar dai sauran musulmai zai zama yana da dukkanin hakkin da ‘yan kasa suke da shi. Bugun mu’assasar da’iratul ma’arif fiKihul  musulunci, wallafar wasu gungun daga malamai, mujallar fiKihun ahlul baiti (as) j 45, shafi 207, Kum, muassar dairatul ma’arif fiKihu islami bisa mazhabar ahlulbait (as) bugu na daya.
[7] Saboda kangare wa umarnin Imam na alkawarin da ya kulla da bazimmen kafiri na zai kare dukiyar sa da ransa da mutuncinsa.
[8] Dabasi najamuddin, na farisance (hukuku zindani wa zindaniyan dar islam) sarul islam, shafi 91, bustani kitab, Kom, bugu na farko. Da kuma shaharudi hashimi sayyid Mahmud a littafinsa na farisanci (bayestahaiye fiKihu), shafi na 275, mizan- mizan,Tehran buguna farko 1419. Littafin farisanci (Zindan da tab’id dar islam) wanda Husaini sayyid Muhammad  Ridha da shafi’i musdafa suka tarjama shafi 38 Kum bugu na farko 1427.
[9] Ta’aziri da ma’anarsa faffada ya hada har da kulle wa a gidan yari ko kurkuku.  
[10](hukuku zindani wa zindaniyan dar islam) shafi 91 da (bayestahaiye fiKihu), shafi na 275 da (Zindan da tab’id dar islam) shafi 38.
[11] Kafirin da bai ya nufin ya yiwa musulmai liken asiri ko yi musu zagon kasa, shi dai kasuwanci ne ya kawo shi a matsayin wakilin wata kasa, kuma ya yi nufin shiga kasar musulmai sai musulmai suka kulla alkawarin aminci da shi za a ba shi hakkin shigowa kasa kuma shi ake cewa kafirin amana. Mujallar fiKihu Ahlulbait (as). J 45 shafi 208.
12 Su ne kafiran da suka kulla alkawari da musulmai kamar yin sulhu, ana kiransu (kafiran yakin) da aka kulla alkawari da su mujallar fiKihu islami Ahlulbait (as).
[13]  mujallar fiKihu islami Ahlulbait (as) (ta larabci) j 24 shafi 17. Da kuma khomaine musawi sayyid  ruhullah a cikin taudhihul masa’il mai (hashiya) wand aka gyara aka yi wa hashiya na khomaini bani hashim, sayyid Muhammad  Husain j 2 shafi 824. Daftari intisharatu islami Kom, 1424. Da zanjani shubaur sayyid Musa a risalatul taudhihul masa’il  shafi 634, Kom, salsabil bugu na farko. 1430. Da kuma kabuli fayyadh Muhammad Dan ishak a cikin risalar taudhihul masa’il shafi 687, Kum majlisi bugu na farko 1426.
TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

Mafi Dubawa