advanced Search
Dubawa
5174
Ranar Isar da Sako: 2012/05/05
Takaitacciyar Tambaya
Me ya sa annabawa (a.s) da ayimmatu Ahlul-bait (a.s), ba su rubuta litattafai da kansu ba?
SWALI
An samu karo da juna cikin litattafan hadisai, me ya sa manzo da ayimmatu Ahlul-bait (a.s) basu rubuta litattafan hadisai da kansu ba a ruwayoyi ? kuma me ya sa basu rubuta tafsiran kurani ba? Wasu manya da dama sunyi litattafai amma mai ya sa ba’a samu daga ayimmatu Ahlul-bait (a.s) ba?
Amsa a Dunkule
Hakika annabin musulunci kari da kudurar Allah (s.w.t) da kaddararsa ya sanya shi bai je makaranta ba kuma bai koyi komai a wajan kowa ba, bashi da malami kuma bai taba rubuta littafi ba .
Hikima cikin wanna kudurkr ta Allah (s.w.t) kuwa a bayyane take, kuma mu’ujizar wannan annabi matabbaciya ita ce alkurani mai girma da aka sani, rubutun littafi da bayyana shi daga wanda ya rubuta zuwa mutane ba ana daukarsa abune marar yiyuwa ba, ko kuma ince a takaice zai iya sanya kokwanto ga wasu domin kuwa shi littafin da mazo yazo da shi ya kai matukar kurewar sanin da dan adam ke tattare dashi wanda wannan kan iya nuna girman sanin manzo bisa ga sauran mutane.
Kuma bamu samu wani daga cikin ayimmatu Ahlul-bait (a.s) ba banda Imama Ali(a.s) da Imam Sajjad (a.s) da ya rubuta littafi ba, kuma wannan ya farune saboda wasu dalilai daban daban, daga ciki akwai nauyin ragamar gudanarwar jagoranci (imamanci) tare da tsayawa da jajircewa kan jama’a, da uzururrukan zamanin kowane imami wadanda su ne mafi muhimmancin gabatarwa bisa ga rubutun littafi, da samun almajiransu marubta litattafai.
Amsa Dalla-dalla
Za’a iya amsa wannan tambayar taku ta hanyoyi daban daban .
1- idan mukayi duba ta mutum takar manzo a kansa, hakika annabin musulunci ya rayune ciki uzururrukan rayuwa na musamman, tare da ikon Allah (s.w.t) da kudurarsa ya sanya manzo baije makaranta ba kuma bai koyi komai a wajan kowane malami ba kuma bai rubuta kowane littafi ba .
Hikima cikin wannan kudurar Allah (s.w.t) kuwa a bayyane take , mu’ujizarsa tabbatacciya ita ce littafi mai girma da aka sani da alkurani, rubuta littafi tare da bayyanar da shi ga wani masani ba ana ganinsa wani abu mara yiyuwa ba, ko kuma ince a takaice zai iya sanya kokwanto ga wasu, domin kuwa shi littafin da mazo yazo da shi ya kai matukar kurewar sanin da dan adam ke tattare da shi wanda wannan kan iya nuna girman sanin manzo bisa ga sauran mutane.
Ta hakane ma muka samu daga littafi mai girma cewa: “Ba ka kasance kana karatun wani littafi ba kafinsa (alkurani) kuma baka rubutunsa da damanka (hannunka), don haka ya auku da masu barna sunyi shakku”[1].
Idan muka yi duba zuwa wannan aya na nuna ana ganin rubutu da karatu ga dan adam na nuna kamalar mutum, amma manzo baya rubutu da karatu wanda ya saba da dabi’un sauran mutane a rayuwa, wanda ya kara hakikancewa kan wannan na daga mu’ujizar annabawa wadda tafi kebantuwa ga cikamakin annabawa (s.a.w), kasancewar karatu da rubutu ya zamo masa babbar mu’ujiza ta wani bangaren, kuma wannan ya kara tabbatar masa cewa shi cikamakin annabawa ne, inda yazo da annabta tare da cikakken sanin hakika da abin da duk tuntnin dan adam ya kunsa majan duk karatu da rubutu, yazo da littafi saukakke daga sama mai tsarki. Ta yadda wadannan uzururruka ke haifar da kokwanto da shakku masu yawa wurin wasu gme da wannan littafin da kuma litattafan da suka damfaru dashi .
Wanda wannan ya gaza zama abin zargi wurin mabiya addinin musulunci, domin manzo bai rubuta komai ba har a lokacin annabtarsa[2], ya kasance yana samun ilimi ne ta hanyar wahayi[3].
2- Me ya sa ayimmatu Ahlul-bait (a.s) basu rubuta littafi ba? Wannan Magana bata inganta ba domin kuwa amirul muminin wanda ake kira da baban ayimmatu Ahlul-bait (a.s) ya rubuta littafi wanda ya’yansa ke kiralittafin (kitabu) Ali(a.s)[4].
Kuma mun samu littafin da aka sani da shifatus sajjadiyya da sakonnin hakkoki (risalatul hukuuk) daga imam Sajjad (a.s), na’am duk da cewa a yau babu wani littafi a wajanmu da muka sani da suna littafin Ali (a.s) wato kitabu Ali(a.s) hakanan dangane da tafsirin al kurani mai girma, amirul muminin shi ne farkon wanda ya fara hada alkur’ani , kuma shi ne wanda ya dauki nauyin sha’anin alkur’ani da fssara wasu daga ayoyi saidai a sannan wato bayan wafatin manzo da ya kawo ba’a karba ba saboda wasu jiga jigan abubuwa da suka faru a farkon musulunci bayan wafatin manzo, ta bangaren halifofi da mutanen da ke bin ra’ayoyinsu[5].
Saidai kuma bayan wadannan litattafan da aka ambata ba’a samu wasu ko wani littafi da wani Imami ya yi ba. Amma wannan na bukatar bayani ta hanyoyi masu zuwa:
  1. Nauyin Imamanci da tsayawar Imamai tsakanin mutane, nauyin abubuwa daban daban da ke wuyan Imamin kowane zamani a lokacinsa, da yake da yawa da nauo’in da ke da matukar daraja ta yadda zai zama yana rubutune daidai da yadda ya dace da aikin mutanensa. domin imami ba marubucin littafi bane kuma ba mawallafi ba, shi kawai ya dukufa wajan bada tarbiyya da imamancin zahiri da na ma’anawiyyar (hakikar) mutane, da aikin tarbiyyantar da dalibansu kubutattu da mujahidai domin su iya bada ransu da sallamawa a tafarkin musulunci. aikin imami ya shafi dukkan lamurran duniya da lahirar mutane ne. wannan lamarin na daga mafi muhimmancin lamura. Saidai dama imami na himmatuwa da aikin da yake shi ne mafi muhimmanci a gareshi, baya yin wani aikin da ba shi ba, saidai bisa gwargwadon girman larura da ta muhimmantar da shi. Irin wannan yanayine tare da damar lokaci ta sanya Imam Ali (a.s) da Imam Sajjad (a.s) suka samu yin litattafai.
  2. Uzururrukan zamani da ta kebanta da shi, wanda shima na da dalilai ta bangarori biyu
  1. Na farko: rashin karbarsu da muhimmantar da su da mutane sukay,i mutane a wancan zamanin sunki muhimmantar da ayimmatu Ahlul-bait (a.s) saboda wasu matsalolin da makiyan ahlul bait (a.s) suke sa musu, mutane basu muhimmantu da ayimmatu Ahlul-bait (a.s) ba muhimmantuwa, wannan abun na hukumomi ya sanyawa mutane rashin kulawa da cire ayimmatu Ahlul-bait (a.s) daga sha’anoninsu, shi ne rahin karbar ayimmatu Ahlul-bait (a.s) da mutane suka yi, wannan rashin muhimmantarwa bazai ragi komai ba daga sha’anin Ahlul-bait (a.s), kuma bazai cutar dasu ba, mutanen da basu karbesu ba su ne suka cutu, duk da cewa kowane hali idan aka samu irin wannan tunani, ra’ayi ko littafi (game da wannan tambayar) amsar na bukatar a duba yanayin zamanin da Imami yake
  2. Na biyu: uzururrukan takiyya a wannan zamani, hakika zurin takiyya wanda yake dddd bawai kawai ya kebantu da abin da ayimmatu Ahlul-bait (a.s) zasu rubuta bane, a’a harma zuwa kan abin da al’umma zasu rubuta. Wani daga daliban Imam Jawad (a.s) ya fadawa Imam cewa “raina fansa a gareka, shehunanamu sun rawaito daga abi Ja’afar da abi Abdullah (imam Bakir da Imam Sajjad (a.s)) takiyya ta yi tsanani a lokacinsu ta yadda suke boye litattafansu ba sa bayyanasu, bayan sun rasu sai muka gada daga garesu. Sai Imam Sajjad ya ce : kuyi aiki dasu domin gaskiyane a cikinsu”[6] . Bugu da kari, da tsananin takiyya ta wanna lokacin ta taka rawa kwarai da gaske wajan rashin rubutun ahlul bait (a.s) (balle ma rubuta littafi ko litattafai) gami da takura musu da masu mulkin abbasiyawa da umayyawa ta kowane mataki (bangare), wanna kan tsananta musu fiye da kima a wasu lokutan , saidai duk da hakan suna iya yin gwargwadon uzurin takiyya, kamar yadda Imama Bakir (a.s) ke cewa “takiyya na daga addini na da addinin iyayena”[7].
  3. Na uku: muhimmantar da rubutun hadisi tare da sanar da mutane ahlul bait (a.s)da yawa daga daliban ahlul bait (a.s) sun tsaya akai, wadanda aka sani da masu rawaito hadisai (muhaddisun), bugu da kari zakaga hadisai da yawa yanzu da muka samu daga wadancen masu hadisan da masu dafa musu, kuma wannan baisa an rasa wannan hadisan ba, wai domin ayimmatu Ahlul-bait (a.s) basu rubutasu ga hannun su ba. Kamar yadda wani ke fadar : da ayimmatu Ahlul-bait (a.s) sun rubuta littafi da kansu, da kuwa an samu sabani a cikinsa, duk da cewa lamarin ba kamar haka bane, shi ne cewar da ayimmatu Ahlul-bait (a.s) sun rubuta littafi da babu damar a canja shi kamar yadda aka yi wa wasu daga wadansu daga dalibansu, domin kuwa kokarin da za’ayi wajan canza litattafan shi ne mafi tsanani kan na dalibansu, kuma zai zama mafi muni wajan batar da mutane idan aka canja littafin kuma da dangantashi mafi girman dangantawa zuwa ga ayimmatu Ahlul-bait (a.s) mafi yawa, domin kuwa mutane harma da masu ruwaya zasu dinga hukunci da litattafan kai tsaye domin ba sa tunani samun wani kuskure da shubuha a ciki don haka dolene su tabbatar an canja ko a’a idan an canja dole ne su dukufa wajan tace ingancinsa da sake duba zuwa garesu (a takaice dai kamar abin da ya faru da hadisan manzo), anan muna ganin babu wata natija na ganin cewa ya kamata ayimmatu Ahlul-bait (a.s) su rubuta littafin tafsiri ko hadisi da kansu, kamar yadda wasu lokutan kukan tambayi ko ku siffanta cewa “karo da juna sunyi yawa cikin litattafan hadisai” wanda hakan baya ingantuwa, e akwai wasu daga dlialai a zahiri da sukazo a hadisai sun nuna hanyoyin warware wadannan mas’aloli ta bangaren malaman musulunci. hadisanmu kamar yadda tarihi ya nuna an tantancesu a lokuta daban-daban tare da dubawa da ingantawa daga wajan sahabban Ayimmatu Ahlul-bait (a.s) da suma kansu (ayimmatu Ahlul-bait (a.s)), wannan bayan abubuwan zahiri na zamani da na cikin wasu ruwayoyin malamai da sukatantance zantukansa.
Domin bukatar bincike da mai zurfi kan hakan kuna iya duba reference kamar haka:
 tambaya ta 3929 (mauki’iy: 4241) ( tantance ingantattun hadisai).
 

[1] Suratu ankabu aya ta 48.
[2] Mudtahhary, murtadha, nabiyyil ummiyyi, page 6, mansharat sadra’a, dadran , 1378HS.
[3] Mukarimush shirazy, Nasir tafsirul amthal bolume 12 page 422, madrasatu Imam Ali (a.s) Kum first edition.
[4] Diwanu Hafiz page 167.
[5] Kulayny Muhammad dan ya’akuub Alkafy bolume 1 page 41 darul kutubul islamiyya Dahran 1365 HS.
[6] Alkafy bolume 1 page 53.
[7] lkafy bolume 2 page 219.
TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

Mafi Dubawa