advanced Search
Dubawa
8968
Ranar Isar da Sako: 2010/11/17
Takaitacciyar Tambaya
mene ne dalilin haramcin marenan raguna?
SWALI
ina son in san mene ne daililin haramcin sayar da marenan rago?
Amsa a Dunkule

Allah madaukaki mai hikima ne, kuma mai hikima  ba ya yin wani aiki da wasa da babu hikima, saboda haka ne duk shi’a suka yi imani da cewa dukkan hukunce-hukunce suna kasancewa bisa maslaha  ne, kuam a wasu wuraren an yi nuni da dalilin haramci a wasu ayoyi da ruwayoyin.

1- Allah madaukaki yana fada a littafin kur’ani mai girma cewa: kuma yana halatta musu dadada…, kuma haka nan hadisan suka zo daga ma’asumai suna karfafa cewa marenan tumaki/awaki suna daga dauda.

2- Imam Sadik (a.s) yana fada cewa: Ibrahim (a.s) an saukar masa da wani rago daga dutsen Sabir wani dutse ne a makka don ya yanka shi, sai iblis ya zo masa ya ce masa: ba ni nawa rabon na wannan ragon? Ya ce: wane rabo kake da shi, alhalin yana matsayin yanka ga ubangijina da fansa ga dana, sai Allah ya yi masa wahayi cewa yana da nasa rabon a ciki, su ne saifa domin shi ne matattarar jini, da marena domin su ne matattarar saduwa kuma magudanar maniyyi, sai Ibrahim (a.s) ya ba shi saifa da marna biyu.

Amsa Dalla-dalla

Tun da cewa Allah madaukaki mai hikima ne[1] wanda babu kuma wani abu na wasa babu dalili[2] da yake faruwa daga mai hikima, don haka ne shi’a suke imani da cewa dukkan hukuncin Allah an shara’nta su ne bisa asasin gyara da kuma barna[3] ne, amma dangane da abin da ake tambaya a kai muna iya nuni zuwa ga misalai biyu daga dalilan wannan haramcin kamar haka:

1- Fadinsa madaukaki a kur’ani mai daraja cewa: “kuma yana halatta musu tsarkaka (dadada), kuma yana haramta musu munana (kazanta) [4].

Kuma bisa zahiri abin da ake nufi da munana a wannan ayar madaukakiya su ne abubuwan da suke da dauda da muni bisa hakika, kuma mai shari’a ya yi bayanin su, a ana nufin duk wani abu da dabi’ar mutum take gudun sa ba ne, domin dabi’ar mutum tana sabawa da sabawar zamani da wuri da yanayi[5].

Sai kuma abu na biyu da ya zo a ruwayoyi; Hakika hadisai sun zo daga ma’asumai (a.s) da suke nuna cewa marena suna daga dauda (kazanta mummuna) ne[6].

2- Saduk yana fada a babi na 357 daga littafin Ilalus shara’i’i game da sirrin haramcin saifa da marna cewa: daga Muhammad Bizandi, daga abana dan usman, ya ce: na ce da abu Abdullah imam Sadik (a.s) yaya kuwa saifa ta zama haram alhalin tana daga abin yanka? Sai ya ce: Hakika Ibrahim (a.s) an saukar masa da rago daga dutsen Sabir wani dutse ne a makka don ya yanka shi, sai iblis ya zo masa ya ce masa: ba ni nawa rabon na wannan ragon? Ya ce: wane rabo kake da shi, alhalin yana matsayin yanka ga ubangijina da fansa ga dana, sai Allah ya yi masa wahayi cewa yana da nasa rabon a ciki, su ne saifa domin shi ne matattarar jini, da marena domin su ne matattarar saduwa kuma magudanar maniyyi, sai Ibrahim (a.s) ya ba shi saifa da marna biyu[7].

 


[1] A Kur’ani akwai wurare 97 da suke bayanin hikimar Allah madaukaki.

[2] Shin kuna tsammanin cewa mun halicce ku da wasa kuma cewa ku ba masu dawaowa ne gare mu ba, muminun: 115.

[3] Don karin bayani game da falsafa sai a koma wa wadannan wurare kamar haka: (hikimar haramta zinare ga maza fayel lamba 2788, (internet 3020) da kuma (hikimar hukuncin fikihu lamba ta 14060 (intanet 13798).

[4] A’arafi: 157.

[5] Majlisi: Muhammad Bakir, biharul anwar, j 59, s 84, mabugar littafin alWafa’, bairut, labnon, shekarar 1404, h k.

[6] Sheikh Saduk, ilalus shara’I, j 2, s 562, gidan yada littafin Addawari Kum; ilalus shara’I – tarjamar attehrani, j 2, s 788, da 789.

[7] ilalus shara’I: j 2, s 562. ilalus shara’I – tarjamar attehrani, j 2, s 788, da 789.

 

TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

  • Da”awar shi”a kan riddar sahabban mazon Allah {s.a.aw} bayan wafatinsa da wacce ma”ana sahabban su ka yi riddar? Shin wannan da”awa za ta iya karbuwa kuwa?.
    12161 Tsohon Kalam 2014/01/27
    samuwar karkata daga nau”in bidi”a da ridda tsakankanin sashen sahabban manzon Allah {s.a.w} bayan wafatinsa. Na farko: daga mahangar littafai na tushe na al”ummar musulmi faruwar hakan wani abu ne da aka sallamawa da babu kokwanto ko shakka ciki sannan kuma sam bai kebantu da littafan shi”a ...
  • Mene ne ma'anar jagorancin malami?
    12834 Sabon Kalam 2012/07/24
    Kalmar Wali da larabci tana da ma'ana guda uku: 1-masoyi, 2-aboki, 3-mataimaki. Bayan haka akwai wasu kalmomi kuma da suke nufin; 1-Salladuwa 2-Jagoranci da shugabanci. "Wilaya" kalma ce da ake amfani da ita da ma'ana biyu a isdilahin fikihu: 1- Wuraren da wanda ...
  • Shin mutum zai iya dawwama; idan haka ne, don me ya sa bai dawwama ba a duniya?
    11634 Sabon Kalam 2012/07/24
    Yana daga abin da yake jan hankli mai kyau a cikin kur’ani mai girma cewa yana ganin mutum wani halitta ne na sama madaukaki mai ‘yanci, kuma wannan jikin nasa ba komai ba ne sai wata sheka ta dan wani lokaci da ruhinsa ya fake a ciki ...
  • Menene hukuncin miji da mata wadanda suke kallon fim din blue fim a tare?
    6979 2018/11/04
    an tambayi daftrorin marja’ai masu alfarma kan tambayar da ka yi kuma ga amsar da suka turo. Ofishin mai girma Ayatullah sayyid Ali Khamna’i (Allah ya tsawaita rayuwarsa): Kalllon finafinai masu tada sha’awa na sa mutun ya karkata zuwa tafarkin shedan na son zuciya kuma yana raunana ...
  • WADAN NE BAITOCI NE ABBAS YAKE RERAWA A LOKACIN DA YA ZO DIBAN RUWA?
    11564 Sirar Manya 2012/07/26
    Mayaka yayin mubaraza a zamanin da su kan yi amfani da wani zaurance (don shaida juna ko ba da sako a tsakaninsu) don haka su kan rera baitotocin waka don samar da karfin gwiwa ga mutanensu da raunana abokan gaba. Imam (a.s) da mutanensa sun yi amfani ...
  • don me ake kiran annabi Muhammad (s.a.w) amintacce?
    6189 تاريخ بزرگان 2019/06/12
    Amintacce shi ne kishiyan mayaudari, watau ana nufin mutumin da ba ya yaudarar jama’a, kuma kowa ya natsu da shi ya dogara da shi bisa kyawun dabi’unsa. Idan muka waiga zuwa ga halayen Annabi (s.a.w) ta mu’amala da daidaku da al’umma tun a samartakarsa, zamu ga amana ...
  • Menene hukunchi namijin da ba ya iya biyawa matarsa hakkokinta?
    14051 2019/06/16
    dawwamar rayuwar aure da karfafarta ya dogara da soyayya da kauna da fuskantar juna da girmama juna. Domin iyali su samu tsayuwa da dawwama Addini Muslunci ya sanya hakkoki ga kowanne dayansu ya kuma ayyana musu wajibai a kansu, duk sa”ilin da aka ce akwai hakkoki to ...
  • Wasu irin hadisai ne suka zo a kan Hukuncin dan zina?
    14544 Dirayar Hadisi 2012/07/25
    Ruwayoyi na musulunci daga annabi (saw) sun yi magana da bayyana hukunce hukuncen dan zina, za mu kawo irin babobinsu Gadon dan zina;- Babin cewa dan zina, shi wanda ya yi zinar ba zai gaje shi ba, da ita mazinaciyar, ko wanda ...
  • Ta wace hanya za mu iya kare kanmu daga kanbun baka?
    26372 Tafsiri 2017/05/20
    Kanbun baka na da tasiri a ruhin mutun wanda babu wani dalili da za a iya kore samuwar sa da shi, ballantana ma an ga faruwar abubuwa masu yawa da suka tabbatar da samuwar kanbun baka ko maita. Marigayi shekh Abbas Kummi ya yi wasici da a ...
  • Shin zai iya yuwuwa a kai ga martabar ubangijintaka?
    8568 Irfanin Nazari 2012/07/25
    Makamin matsayin ubangijintaka yana da matakai da marhaloli mabambanta, kuma don a samu wannan amsar dole ne a ga dukkan martabobi da ma’anonin baki daya. Idan abin da ake nufi da kai wa matakin ubangijintaka shi ne zatin mutum ta canja da sauyawar abin halitta ya koma ...

Mafi Dubawa