advanced Search
Dubawa
16633
Ranar Isar da Sako: 2018/10/01
Takaitacciyar Tambaya
ya zamanin hallitar annabi Adam (a.s) kusan shekaru 5764 a baya zamu kwatanta su da kasusuwan da a ka samu na mutanen da suka rayu sama da {shekara miliyan 25}?
SWALI
daga lokacin zuwan annabi Adam a doran kasa zuwa yau shekaru 5764 ke nan. Tsofafin kasusuwan da a ka samu a doran kasa na mutanen da a wannan zamani yana komawa ga shekaru miliyan 25 da suka wuce, ka ba da amsa tare da dalilai.
Amsa a Dunkule
: ba wani matsala tsakanin wadannan abubuwa biyu. In da za a ce hallitar Adam yana kamawa kusan shekaru dubu shida ko bakwai da suka wuce. mai yiyuwa ne a nan ana nuni da cewa sabuwar hallitar mutum ne, don haka ba mamaki kafin wannan lokaci an hallici mutane da dama a shekaru masu yawa da suka wace kuma ya zamo ba ba su a doran kasa. Akwai alamomi masu yawa da ke nuni da cewa kafin hallitar annabi Adam (a.s) wasu mutane sun rayu kuma ba su cikin zuriyar annabi Adam (a.s).
Koyarwar addini da wasu ruwayoyi na musulunci na nuni da hakan
Amsa Dalla-dalla
Ba wani matsala tsakanin wadannan abubuwa biyu. In da za a ce halittar Adam yana kamawa kusan shekaru dubu shida ko bakwai da suka wuce. Mai yiyuwa ne a nan ana nuni da cewa sabuwar halittar mutum ne, don haka ba mamaki kafin wannan lokaci an halicci mutane da dama a shekaru masu yawa da suka wuce kuma ya zamo babu su a doran kasa. Akwai alamomi masu yawa da ke nuni da cewa kafin halittar annabi Adam (a.s) wasu mutane sun rayu kuma ba su cikin zuriyar annabi Adam (a.s).
Koyarwar addini da wasu ruwayoyi na musulunci na nuni da hakan[1].
Allama tabataba'i a cikin suratul nisa aya ta daya yana cewa: ayar a fili tana nuna cewa {nafsi wahid} ana nufin Adam sai {zaujiha} kuma a na nufin hauwa wanda su ne iyayan mutane wanda muka fito daga cikin su[2], zamu iya gane cewa ayar na nuni da cewa dukkan mutane asalin su daga wadannan mutum biyun ya ke wato Adam da hauwa. A fili ya ke ayar na nuni da cewa mutane da ke rayuwa a doran kasa yanzu asalin su Adam ne da hauwa, wadannan mutum biyun su ne kadai suka yada zuriyar dan Adam a doran kasa.
A cikin tarihin yahudawa ya zo cewa daga lokacin da a ka halitta dan Adam adoran kasa zuwa yau kimanin shekaru dubu bakwai kenan hankalima zai iya gasganta hakan. Wato a hankalce za a iya cewa halittar bata wuce wadannan shaikarun ba. Sai dai masana ilimin kasa suna ganin cewa irin mutum ya kai sama da miliyoyin shekaru da suka wuce.
A mahankar su ke nan, amma sai dai dalilan baya da da wani inganci wanda zai tabbatar da cewa duddugar kasusuwan da masu bincike suke samowa a cikin kasa na nufin cewa asalin kakanin mutanen wannan zamanin ne, kuma ba wani dalili da zai kore cewa kasusuwan da a ke samawa ba na mutanen da suka zauna doran kasa kafin dan Adam ba, saboda mai yiyuwa ne hakan ta faru wato wasu halitu na mutane kafin wadannan na yanzu sun zauna a doran kasa, wanda ba wani alaka a tsakani wadan nan hallitu biyu. Mai yiyuwa ne wasu matane kafin hallitar annabi Adam sun rayu a doran kasa kuma ya zaman to zuriyar su ta kare, da haka samuwar hallitar mutane ta zama wasu su zo su wuce har zuwa zamani hallitar Adam.
Kur’ani mai girma baiyi bayani a fili cewa ya samuwar mutane ta zamo ba shin bayyanar mutane a doran kasa ya takaita ne kawai da wannan al'ummar da muke ciki kadai, ko kuwa an yi zamani da dama ana hallitu suna wuce wa har zuwa lokacin yau, shin al'ummar yanzu su ne karshen hallitu?
Mai yiyuwa ne a wasu ayoyin na Kur’ani sun yi nuni da cewa kafin hallitar Adam wanda shi ne baban mutane an yi wasu mutane a doran kasa kamar yadda yake cewa: a zamani da Allah madaukaki ya ce da mala'iku zan sa madadina a bayan kasa sai suka ce kamar ya zaka sake sa masu barna da zubar da jini a doran kasa. [3]
Allama tabataba'i ya ce: suratul bakara aya ta 30 zamu iya fahimtar cewa kafin hallitar Adam wasu matane sun rayu wanda ya sa mala'iku suka tambayi Allah a kan sake hallitar masu barna da zubar da jini domin mala'ikun sana da sani a kan aikin da wannan hallitu suka aikata[4].
Wannan ayar na nuni da cewa kafin hallitar Adam wani zamani ya faru wanda mutane suka zauna a doran kasa kuma mala'iku su ka ga abin da suka yi na barna da zubar da jini.
A cikin wasu ruwayoyi na imamai (a.s) akwai wasu abubuwa da ke nuni cewa kafin mutanen wannan zamani an yi wasu mutanen daban.
Sheikh saduk a cikin littafin tauhid ya rawaito daga imam sadiq (a.s) cewa: shin abin mamaki ne a kare ku cewa Allah madaukaki ya yi wasu matane ba ku ba? A 'a bahaka ba ne, an dai hallita dubanin mutane wanda ku ne karshen su[5].
Marikayi suduk a cikin littafin khasal, daga imam bakir (a.s) ya rawaito cewa: ranar da Allah madaukaki ya halitta duniyoyi bakwai {sannan ya gama da su} dukkan wadannan duniyoyin babu daya wadda zuriyar Adam suka zauna a ciki Allah madaukaki ya hallita wannana duniyoyi kuma ya sa zuriya bayanzuriya kowace zuriya ya hallita mata duniyar ta daban, wanda daga karshe a ka hallita Adam baban mutanen wannan zamani wanda daga gare shi ne al'umma da yadu. [6]،[7]
A bisa haka ne, za a ce da za a samu sauran wani abu wanda ke nuni da wasu hallitu wadanda suka rayu sama da miliyoyin shekaru to wannan baya na nufin cewa ya shafi hallitar mutanen yanzu ba ne domin, a fili ya ke cewa hallitar annabi Adam (a.s) bai wuce shekaru 7000 ba[8].
Karin bayani a duba tambaya lamba ta: 506. Da kuma lamba ta: 731.
 

[2] Tarjamar almizan jildi na 4,shafi na 214,qom, bugawa ofishin yada musulunci,1417.
[3] Bakara 30.
[4] Tarjamar mizan jildi na 4, shafi na 223.
[5] Shaikh suduk, tauhid ,shafi na 277, jildi na 2,bugun Tehran.
[6] Sheikh suduk, khasal, jildi na 2, shafi na 652, jildi na 54.
[7] Daga fuyiko fursiman kur'ani.
[8] A na iya dubawa cikin{sayit tambaya da 701} shekarun nau'I mutum cikin kur'ani.
 
 
 
TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

  • menene hakikanin ma’anar salla?
    36439 Halayen Aiki 2012/07/25
    Salla daukakace ga duk mai san daukaka, ita ce hanya kai tsaye ba tare da shamaki ba, domin ita ce ganawa da ubangiji. Kamar yadda ya zo a Kur'ani mai girma cewa “hakika ni ne ALLAH wanda ba wani ALLAH sai ni to ku bauta ...
  • mece ce alakar jagorancin malami da jam'iyyu?
    7110 Tsare-tsare 2012/07/24
    Kungiyoyin siyasa, da ma'anar wasu jam'iyyu masu iri-iri akwai su a cikin kowace al'umma tun zamanin da. A yanzu ana ganin jam'iyyun siyasa a matsayin wani abu na tarayyar mutane da 'yancin zabe ne. bisa wannan asasin ne ya zama dole mu kalli wannan lamari a matsayin ...
  • Shin zai yiwu ai mana bayanin tafsirin suratu kausar?
    15332 Tafsiri 2017/06/17
    Suratu kausar sura ce da take da ayoyi guda uku, abin da ya fi shahara gun malamai shi ne an sauke ta a garin makka; sannan dalilin saukar ta shi ne yayewa manzon rahama (s.a.w) damuwar da yake ciki sakamakon mauta da gorin da wasu cikin kuraishawa ...
  • Ta yaya za a magance matsala, idan lamarin na hankali ya ci karon da na addini?
    14504 Sabon Kalam 2012/09/16
    Hankali shi ne hujjar Allah ta addini wacce ya ba wa mutum, hankali ke yi wa mutum jagora har ya kai shi ga samun cikakkiyar kamala, Shari`a hujja ce ta fili wacce take hana mutum gurbata da cutaya kuma ta kai shi ga samun cika da rabauta. ...
  • shin Imamul hujja a tsibirin bamuda yake zaune?
    15739 تاريخ بزرگان 2012/07/25
    Dalilin da ya sa wasu mutane suka yi ammanar cewa “Tsibirin Bamuda shi ne mazaunar Imamu Mahdi (a.s), gani suke Tsibirin Bamuda shi ne “Jazijrayul Khadra’a”. Bisa kaddara cewa Jaziratuk Khadra’a ita ce mazaunar Imamu Mahdi (a.s) shi ya sa suka ce Tsibirin Bamuda ya kunshi wadannan ...
  • Yaya aka samu sauyi a addinin Kiristanci, kuma da wane dalili ne ya samu karkacewa da jirkicewa
    12699 Sabon Kalam 2012/07/23
    Yayin da masu biyayya ga addinin Isa (a.s) suka haramata wa kawukansu wannan ni'ima ta samuwarsa a cikinsu, har ya samu hawa zuwa sama, sai manzanninsa da 'yan sakonsa suka ci gaba d aisar da sakonsa, kuma suka fuskanci wahalhalu masu yawa a kan hakan.
  • An lura da cewa Kur’ani mai girma shi ne mu’ujizar cika makin Manazannin Allah, to meye fuskokin gajiyarwar (kalu balen) da ke akwai a cikinsa?
    16211 Ilimin Kur'ani 2012/07/25
    An ambaci fuskokin gajiyarwar (kalu balen) da Kur’ani mai girma ya yi wadda zai yiwu na ambaci uku daga ciki: Ya gajiyar ta bangaren yare da bayani Ya gajiyar da fuskacin abin da ya kunsa Sannan kuma ya gajiyar ta ...
  • menene dalili a kan tabbatar shugabancin malami.
    18045 Hakoki da Hukuncin Shari'a 2012/07/26
    Akwai hanyoyi mabanbanta domin tabbatar da “shugabancin malami” sai dai a nan za mu isu da ambaton dalilai guda biyu na hankali da na ruwaya domin tabbatar da ita. Dalili na hankali: Hankali ya tabbatar da wajabcin samun mutumin da ke ...
  • Ta wace Hanya ake mangance maita da kanbun baka?
    40482 Halayen Aiki 2017/05/21
    Lalle Alkura'ani ma ya tabbatar da akwai maita, inda ya nuna wasu alamu da suke gaskata abin da tarihi ya tabbatar na daga cikin abin da Al’kur'anin ya zo da shi na daga al’umman da suka shude. Wasu malamai a wannan zamanin suna ganin wasu daga cikin ...
  • Menene hukunchi namijin da ba ya iya biyawa matarsa hakkokinta?
    13746 2019/06/16
    dawwamar rayuwar aure da karfafarta ya dogara da soyayya da kauna da fuskantar juna da girmama juna. Domin iyali su samu tsayuwa da dawwama Addini Muslunci ya sanya hakkoki ga kowanne dayansu ya kuma ayyana musu wajibai a kansu, duk sa”ilin da aka ce akwai hakkoki to ...

Mafi Dubawa