advanced Search
Dubawa
5907
Ranar Isar da Sako: 2012/05/05
Takaitacciyar Tambaya
don me ake kiran annabi Muhammad (s.a.w) amintacce?
SWALI
don me ake kiran annabi Muhammad (s.a.w) da Muhammad amintacce?
Amsa a Dunkule
Amintacce shi ne kishiyan mayaudari, watau ana nufin mutumin da ba ya yaudarar jama’a, kuma kowa ya natsu da shi ya dogara da shi bisa kyawun dabi’unsa. Idan muka waiga zuwa ga halayen Annabi (s.a.w) ta mu’amala da daidaku da al’umma tun a samartakarsa, zamu ga amana wata dabi’a ce da ta samu gindin zama a gun sa saboda ya Shahara da gaskiya da amana a tsakanin mutane kana kowa ya natsu da shi, wannan ya sa ake kiran sa da “Al’amin”.
Abin da yake da muhimmanci mu fadi a nan shi ne bayan kasantuwar Annabi (s.a.w) aminin wahayin Allah ne, abin dogaro ne a gun Allah (s.a.w) kamar yadda ya kasance a gun jama’a.
A addu’o’i na ziyarar Annabi (s.a.w) kamar yadda aka ruwaito daga Ma’asumai (a.s) sun zo da lafuza Kalmar “Aminullahi” a gurare da dama. Kana dimbin ruwayoyi da suka zo da wannan lakabi suna da damar gaske, wadda hakan zai kara tabbatar da abin da muke zance a kai.
Amsa Dalla-dalla
Amintacce shi ne kishiyan mayaudari, watau ana nufin mutumin da ba ya yaudarar jama’a, kana kowa ya natsu da shi ya dogara da shi bisa kyan dabi’unsa[1]. Idan muka waiga zuwa ga halayen Annabi (s.a.w) wajen mu’amala da daidaku da kuma al’umma tun a samartakarsa,1 zamu ga wata dabi’a ce da ta samu gindin zama a gun sa saboda ya Shahara da gaskiya da amana a tsakanin mutane kana kowa ya natsu da shi, shi ya sa a ke kiransa da “Al’amin”.
An ruwaito cewa wani ayari na fatake da ya bar Makka ya tafi Basara da ke kasar Sham don yin kasuwanci, sun tadda wani fasto na jiran ayarin. Suna isa sai ya tambaye su; A cikin masu aikin hajji na wannan shekara akwai mutanen Makka? Sai suka ce: “Akwai”. Sai ya ce: “To ku tambaya Ahmad bin Abdulmudallib ya bayyana? Domin a wannan watan zai bayyana, kuma shi ne Annabin karshe”. Mai ruwayar ya ce: “Da na dawo Makka sai na tambaya me ya faru”? Sai suka ce: “Muhammad bin Abdullah Al’amin[2] ya yi da’awar Annabta”[3].
Abin da yake da mahimmanci mu fadi a nan shi ne bayan kasantuwar Annabi (s.a.w) aminin wahyin Allah ne, abin dogaro gun Allah (s.a.w) kamar yadda ya kasance a gun jama’a. Wannan shi ne dalilin kiransa da “Al’amin” kamar yadda ya zo a Kur’an da kuma hadisai. Kana Annabi ba ya da bambanci da sauran annabawa, domin duka annabawa amintattu ne na wahayin Allah (s.w.t). Shi ya sa Allah ke fada a kissar Annabi Hudu (a.s) Ya ke cewa: “Isar muku nake da sakonnin Ubangijina kuma ina mai muku nasiha ne amintacce. ”3. Kamar yadda Kur’ani Mai Girma ya kawo a bisa harshen Annabi Nuhu da Annabi Ludu da Annabi Salihu da Annabi Shu’aibu (a.s) kowanne sai da ya cewa jama’arsa: “Hakika ni, manzo ne amintacce”[4].
Akwai gurare da dama a addu’o’in ziyarar Annabi (s.a.w) da Ma’asumai suka ruwaito mukan kira Annabi da Kalmar “Aminulallah”. Daga cikinsu akwai inda muke zantawa da shi a wasu ziyzrce-ziyarce muna cewa “Assalumu alaika ya rasulallah (s.a.w) Muhammadu Aminullahi wa ala rusuliHi wa aza’imi amriHi…”[5]. Ruwayoyi sun yawaita zuwa da wannan a gurare da dama, zamu kawo guri daya don ba da misali:
 An karbo daga Abdullahi bin Jundub yana cewa: Imamu Rida (a.s) ya rubuta wasika zuwa gare ni ya ce: “Bayan haka, hakika Allah Ya aiko Muhammadu (s.a.w) ya kasance Aminin Allah a halittarSa, bayan kauransa sai mu Ahlul baiti muka gaje shi mu ne amintattu na Allah a bayan kasarSa”[6].
 

[1] Almuhaiyir, Rida, Almu’ajam Al’abajadi (Arabi-Farisi) sh4.
[2] Arruwandi, Kudubuddin, Alkhara’ij j1, sh125-126, wal Jawarih, Mu’assatul Imamu ul Mahdi (AJ) Kum, 1409 K.
[3] Al’a’raf: 68.
[4] Ashu’ara: 107,125’143’ 162’ 178.
[5] Ibinkulkwaih Alkummi, Kamiluzziyara’at, sh 201. dabaa’in IntiShara’at murtadyah, Najafui Ashraf,1365,H.
[6] Alkulaini, Muhammad bin yakub, Alkafi, j1, sh223, Darulkutub Al-islamiyah,Tehran, 1365, H.
TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

  • menene hakikanin ma’anar salla?
    36439 Halayen Aiki 2012/07/25
    Salla daukakace ga duk mai san daukaka, ita ce hanya kai tsaye ba tare da shamaki ba, domin ita ce ganawa da ubangiji. Kamar yadda ya zo a Kur'ani mai girma cewa “hakika ni ne ALLAH wanda ba wani ALLAH sai ni to ku bauta ...
  • mece ce alakar jagorancin malami da jam'iyyu?
    7110 Tsare-tsare 2012/07/24
    Kungiyoyin siyasa, da ma'anar wasu jam'iyyu masu iri-iri akwai su a cikin kowace al'umma tun zamanin da. A yanzu ana ganin jam'iyyun siyasa a matsayin wani abu na tarayyar mutane da 'yancin zabe ne. bisa wannan asasin ne ya zama dole mu kalli wannan lamari a matsayin ...
  • Shin zai yiwu ai mana bayanin tafsirin suratu kausar?
    15332 Tafsiri 2017/06/17
    Suratu kausar sura ce da take da ayoyi guda uku, abin da ya fi shahara gun malamai shi ne an sauke ta a garin makka; sannan dalilin saukar ta shi ne yayewa manzon rahama (s.a.w) damuwar da yake ciki sakamakon mauta da gorin da wasu cikin kuraishawa ...
  • Ta yaya za a magance matsala, idan lamarin na hankali ya ci karon da na addini?
    14504 Sabon Kalam 2012/09/16
    Hankali shi ne hujjar Allah ta addini wacce ya ba wa mutum, hankali ke yi wa mutum jagora har ya kai shi ga samun cikakkiyar kamala, Shari`a hujja ce ta fili wacce take hana mutum gurbata da cutaya kuma ta kai shi ga samun cika da rabauta. ...
  • shin Imamul hujja a tsibirin bamuda yake zaune?
    15739 تاريخ بزرگان 2012/07/25
    Dalilin da ya sa wasu mutane suka yi ammanar cewa “Tsibirin Bamuda shi ne mazaunar Imamu Mahdi (a.s), gani suke Tsibirin Bamuda shi ne “Jazijrayul Khadra’a”. Bisa kaddara cewa Jaziratuk Khadra’a ita ce mazaunar Imamu Mahdi (a.s) shi ya sa suka ce Tsibirin Bamuda ya kunshi wadannan ...
  • Yaya aka samu sauyi a addinin Kiristanci, kuma da wane dalili ne ya samu karkacewa da jirkicewa
    12699 Sabon Kalam 2012/07/23
    Yayin da masu biyayya ga addinin Isa (a.s) suka haramata wa kawukansu wannan ni'ima ta samuwarsa a cikinsu, har ya samu hawa zuwa sama, sai manzanninsa da 'yan sakonsa suka ci gaba d aisar da sakonsa, kuma suka fuskanci wahalhalu masu yawa a kan hakan.
  • An lura da cewa Kur’ani mai girma shi ne mu’ujizar cika makin Manazannin Allah, to meye fuskokin gajiyarwar (kalu balen) da ke akwai a cikinsa?
    16211 Ilimin Kur'ani 2012/07/25
    An ambaci fuskokin gajiyarwar (kalu balen) da Kur’ani mai girma ya yi wadda zai yiwu na ambaci uku daga ciki: Ya gajiyar ta bangaren yare da bayani Ya gajiyar da fuskacin abin da ya kunsa Sannan kuma ya gajiyar ta ...
  • menene dalili a kan tabbatar shugabancin malami.
    18045 Hakoki da Hukuncin Shari'a 2012/07/26
    Akwai hanyoyi mabanbanta domin tabbatar da “shugabancin malami” sai dai a nan za mu isu da ambaton dalilai guda biyu na hankali da na ruwaya domin tabbatar da ita. Dalili na hankali: Hankali ya tabbatar da wajabcin samun mutumin da ke ...
  • Ta wace Hanya ake mangance maita da kanbun baka?
    40482 Halayen Aiki 2017/05/21
    Lalle Alkura'ani ma ya tabbatar da akwai maita, inda ya nuna wasu alamu da suke gaskata abin da tarihi ya tabbatar na daga cikin abin da Al’kur'anin ya zo da shi na daga al’umman da suka shude. Wasu malamai a wannan zamanin suna ganin wasu daga cikin ...
  • Menene hukunchi namijin da ba ya iya biyawa matarsa hakkokinta?
    13746 2019/06/16
    dawwamar rayuwar aure da karfafarta ya dogara da soyayya da kauna da fuskantar juna da girmama juna. Domin iyali su samu tsayuwa da dawwama Addini Muslunci ya sanya hakkoki ga kowanne dayansu ya kuma ayyana musu wajibai a kansu, duk sa”ilin da aka ce akwai hakkoki to ...

Mafi Dubawa