advanced Search
Dubawa
9184
Ranar Isar da Sako: 2012/05/14
Takaitacciyar Tambaya
Shin hadisin da ke cewa “duk wanda ya mutu ba shi da bai’ar imamin zamaninsa (Imaminsa) ya yi mutuwar jahiliyya” daga manzo (s.a.w) yake kuwa?
SWALI
Akwai rawaitaccen hadisi daga sunna cewa “duk wanda ya mutu ba shi da bai’ar imami zamaninsa (Imaminsa) ya yi mutuwar jahiliyya” a fili yake cewa wannan hadisi na nuna muhimmancin bai’a, shin manzo (s.a.w) ya yi wannan magana ne ba tare da nufin a yi mubayi’a ga wani ba? Kuma sannan me ya sa manzo (s.a.w) bai ce a yi bai’a ga wani bayansa ba? Kamar yadda Ahlus sunna ke fada.
Amsa a Dunkule

Bai’a na da bangarori biyu, mai bai’a (sauran mutane) da wanda ake yi wa bai’ar (wato su ne manzo (s.a.w) da imamai (a.s)). Tare da cewar manzo (s.a.w) shi ne hujja kuma shugaba, don haka shi za a yiw mubayi’a a matakin farko wato shi ne farkon wadanda za a yi wa mubayi’a ba shi zai yita ga waninsa ba, ruwayoyi da suka zo daga litattafan shi’a sun karfafa hakan Kamar yadda mai tambaya ya kawo, kuma babu makawa cewa ruwayoyin ba wai kawai kara zube ba wanda da ansan hakan shi ke nan, a’a, bin hanyar tare da tafiya akai shi ne ainihin abin nufi wato bin manzo (s.a.w) ko Imamin zamani lokacin da yake raye.

Akan wannan ne nake cewa shi hadisin bawai kawai an rawaito cewa ai manzo (s.a.w) shi ne farkon wanda za a yi wa bai’a ba, da sunan wanda aiki ya fada a kansa ba (fa’ili) ba kuma shi ne mai yi wa wani ba (maf’uul). Amma idan muka dubi dangantakar hadisin da nuni kan sanya halifa a bayan manzo (s.a.w) a ban kasa wanna ya tabbata tare da dalilai masu yankan shakku cewa manzo (s.a.w) ya sanya Imam Ali (a.s) halifansa bayansa, wannan mun yi bayaninsa sosai ciki mafiya yawan tambayoyi, duba nan kasa ciki bayani a fayyace.

Amsa Dalla-dalla

Amsa wannan tambaya na bukatar bayanin wasu lamurra kamar

  1. Ma’anar bai’a
  2. Matsayin manzo (s.a.w) cikin al’ummar musulmi
  3. Rawaitattun ruwayoyi daga Ahlul-baiti (a.s) kan wajabcin sanin imamain zamani

1-MA’ANAR BAI’A

A Kalmar larabci bai’a na nufin cinikayya, sun kasance idan akabi manzo (s.a.w) ko Imami suka karba daga wajansa, shi kuma ya ba su tare da karfafarsu, ya yi kama da aikin mai saye da siyarwa.

 Amma a ma’ana ita bai’a wani sanannen alkawari ne ake yi wa manzo (s.a.w) ko imamin zamani wajan mika masa wuka da nama cikin kowane lamari ba tare da jayayya ba.[1]

Daga nan zamu kara gane cewa ita bai’a na da bangarori biyu bangaren farko shi ne ke bayyana bangare na biyu, kuma bangaren farko shi ne wanda ake yi wa mubayi’a (manzo (s.a.w)da Imami) bugu da kari manzo (s.a.w) shi ne ma’auni mai shiryarwa kuma shugaba, wanda shi ne ma’aikin da aka aiko kuma imami kama yadda ya zo a kur’ani “Muhammad bai kasance uban kowaba daga mazajenku sai da shi ya kasance …[2].

Wannan aya na nuna manzo (s.a.w) shi za a yi wa bai’a bawai shi ne zai yi wa wani ba (shi ne mai siyarwa ba wai mai siye ba)ta haka ne muka samu kur’ani na yi mana magana bisa waccen bai’ar (siyarwar) kamar yadda ya kara da cewa “lallai wadannan da suka yi maka mubayi’a, ba kai suka yi wa ba sun yi wa Allah (SW) ne …”.[3] da kuma fadin sa madaukakin sarki cewa “hakika Allah (SW) ya yarda da muminai da suka yi maka mubayi’a …”.[4]  wannan na karfafar litattafan da aka rawaito daga litattafan shi’a cewa duk wanda bai san imamin zamaninsa ba ya yi mutuwar jahiliyya “idan ya mutu bai san Imamin zamaninsa ba ya yi mutuwar jahiliyya”.[5] sanin hadisin ba wai shi ne muhimmi ba, bin hanyar da take ita ce zakasan Imamin zamaninka shi ne manzo (s.a.w) ko Imaminka a lokacinsa, akan wannan ne hadsin baya nufin manzo (s.a.w) ne mai bi ba, a’a shi ne wanda za a bi da sifar wanda aiki ya fada a kansa, ba wai a sigar mai aiki ba.

 


[1] majlisy Muhammad Bakir, mirathul ukuul cikin sharhin akhbar aali Muhammad bolume 20 page 356, darul kutubul islamiyya, bugu na biyu tdahran Iran 1404 AH

[2] suratul ahzab, 40

[3] suratu fat’hi, 10

[4] suratu fat’hi 18

[5] hurrul Aamily, Wasailush shi’a bolume 16 page 246, yadawar mu’assasatu ahlul bait (a.s)

 

TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

  • menene hakikanin ma’anar salla?
    36439 Halayen Aiki 2012/07/25
    Salla daukakace ga duk mai san daukaka, ita ce hanya kai tsaye ba tare da shamaki ba, domin ita ce ganawa da ubangiji. Kamar yadda ya zo a Kur'ani mai girma cewa “hakika ni ne ALLAH wanda ba wani ALLAH sai ni to ku bauta ...
  • mece ce alakar jagorancin malami da jam'iyyu?
    7110 Tsare-tsare 2012/07/24
    Kungiyoyin siyasa, da ma'anar wasu jam'iyyu masu iri-iri akwai su a cikin kowace al'umma tun zamanin da. A yanzu ana ganin jam'iyyun siyasa a matsayin wani abu na tarayyar mutane da 'yancin zabe ne. bisa wannan asasin ne ya zama dole mu kalli wannan lamari a matsayin ...
  • Shin zai yiwu ai mana bayanin tafsirin suratu kausar?
    15332 Tafsiri 2017/06/17
    Suratu kausar sura ce da take da ayoyi guda uku, abin da ya fi shahara gun malamai shi ne an sauke ta a garin makka; sannan dalilin saukar ta shi ne yayewa manzon rahama (s.a.w) damuwar da yake ciki sakamakon mauta da gorin da wasu cikin kuraishawa ...
  • Ta yaya za a magance matsala, idan lamarin na hankali ya ci karon da na addini?
    14504 Sabon Kalam 2012/09/16
    Hankali shi ne hujjar Allah ta addini wacce ya ba wa mutum, hankali ke yi wa mutum jagora har ya kai shi ga samun cikakkiyar kamala, Shari`a hujja ce ta fili wacce take hana mutum gurbata da cutaya kuma ta kai shi ga samun cika da rabauta. ...
  • shin Imamul hujja a tsibirin bamuda yake zaune?
    15739 تاريخ بزرگان 2012/07/25
    Dalilin da ya sa wasu mutane suka yi ammanar cewa “Tsibirin Bamuda shi ne mazaunar Imamu Mahdi (a.s), gani suke Tsibirin Bamuda shi ne “Jazijrayul Khadra’a”. Bisa kaddara cewa Jaziratuk Khadra’a ita ce mazaunar Imamu Mahdi (a.s) shi ya sa suka ce Tsibirin Bamuda ya kunshi wadannan ...
  • Yaya aka samu sauyi a addinin Kiristanci, kuma da wane dalili ne ya samu karkacewa da jirkicewa
    12699 Sabon Kalam 2012/07/23
    Yayin da masu biyayya ga addinin Isa (a.s) suka haramata wa kawukansu wannan ni'ima ta samuwarsa a cikinsu, har ya samu hawa zuwa sama, sai manzanninsa da 'yan sakonsa suka ci gaba d aisar da sakonsa, kuma suka fuskanci wahalhalu masu yawa a kan hakan.
  • An lura da cewa Kur’ani mai girma shi ne mu’ujizar cika makin Manazannin Allah, to meye fuskokin gajiyarwar (kalu balen) da ke akwai a cikinsa?
    16211 Ilimin Kur'ani 2012/07/25
    An ambaci fuskokin gajiyarwar (kalu balen) da Kur’ani mai girma ya yi wadda zai yiwu na ambaci uku daga ciki: Ya gajiyar ta bangaren yare da bayani Ya gajiyar da fuskacin abin da ya kunsa Sannan kuma ya gajiyar ta ...
  • menene dalili a kan tabbatar shugabancin malami.
    18045 Hakoki da Hukuncin Shari'a 2012/07/26
    Akwai hanyoyi mabanbanta domin tabbatar da “shugabancin malami” sai dai a nan za mu isu da ambaton dalilai guda biyu na hankali da na ruwaya domin tabbatar da ita. Dalili na hankali: Hankali ya tabbatar da wajabcin samun mutumin da ke ...
  • Ta wace Hanya ake mangance maita da kanbun baka?
    40482 Halayen Aiki 2017/05/21
    Lalle Alkura'ani ma ya tabbatar da akwai maita, inda ya nuna wasu alamu da suke gaskata abin da tarihi ya tabbatar na daga cikin abin da Al’kur'anin ya zo da shi na daga al’umman da suka shude. Wasu malamai a wannan zamanin suna ganin wasu daga cikin ...
  • Menene hukunchi namijin da ba ya iya biyawa matarsa hakkokinta?
    13746 2019/06/16
    dawwamar rayuwar aure da karfafarta ya dogara da soyayya da kauna da fuskantar juna da girmama juna. Domin iyali su samu tsayuwa da dawwama Addini Muslunci ya sanya hakkoki ga kowanne dayansu ya kuma ayyana musu wajibai a kansu, duk sa”ilin da aka ce akwai hakkoki to ...

Mafi Dubawa