advanced Search
Dubawa
15868
Ranar Isar da Sako: 2012/04/04
Takaitacciyar Tambaya
Idan aka yi la’akari da ka’idar cewa duniya ba ta zama ba tare da hujjar Allah madaukaki a cikinta ba, shin wane ne hujja a tsakanin lokacin hawan saman annabi Isa (a.s) da lokacin tayar da annabi (s.a.w) ?
SWALI
Idan aka yi la’akari da ka’idar cewa duniya ba ta zama ba tare da hujjar Allah madaukaki a cikinta ba, wanda shi ne imami ma’asumi. Wannan shi ne abun da hujjar hankali ta tabbatar a cikin bincike game da akidar imamanci, shin wane ne hujja a tsakanin lokacin hawan saman annabi Isa (a.s) da lokacin tayar da annabi (s.a.w) ?
Amsa a Dunkule

Yana inganta a samu tazara a tsakanin annabawa masu shari”a, wato a aiko wani annabi kafin shekara dubu, sai wani annabin ya zo bayansa acikan shekara dubun, kuma wannan mas’alar ba ta warware hadisan da suke karfafa cewa ita duniya ba ta zama ba tare da hujjar Allah a cikinta ba, domin hujjar Allah da ake nufi ya shafi annabawa da imamai da halifofin annabawan.

 Hakika ya zo a cikin hadisai cewa duniya ba ta zama ba tare da hujjar Allah ba, wanda zai tsaya da hujjar Allah, ko dai wanda yake a fili a sarari sananne, ko wanda yake a boye a cikin tsoro, don kada hujjojin Allah da dalilansa su rushe.kuma ishara tazo a cikin hadisai a kan hujjojin Allah bayan annabi Isa (a.s) tun daga sham’un dan hamunis safa har ya kare da imamul hujja (A.T.F).

Amsa Dalla-dalla

Yana inganta a samu tazara a tsakanin annabawa masu shari’a, wato aiko wani annabi kafin shekara dubu, sai wani annabin ya zo bayan sa a cikan shekara dubun, kuma wannan mas’alar ba ta warware hadisan da suke karfafa cewa ita duniya ba ta zama ba tare da hujjar Allah a cikinta ba, sai dai ba ya inganta a ce kwata-kwata babu shi hujjar Allah din, a ce a duniya babu shi.

 A saboda haka a bisa lalura wajibi ne ya zamo akwai hujjar Allah a kowane lokaci da zamani don duniya ta iya wanzuwa da shi, ko dai wanda yake a fili a sarari sananne, ko wanda yake a boye a cikin tsoro”.

 Akwai wasu hadisai da suka yi nuni ga jerin sunayen halifofi da annabawa bayan annabi isa (a.s) har zuwa wannan lokacin namu, su ne: sham’un dan hamunissafa, shi kuma sham’un ya yi wasiyya ga yahaya dan zakariyya, shi kuma yahaya dan zakariyyaya ya yi wasiyya zuwa ga munzir, shi kuma munzir ya yi wasiyya zuwa ga sulaimat, shi kuma sulaimat ya yi wasiyya ga burdat, zuwa ga annabi (s.a.w) annabi ya yi wasiyya ga ali har wasiccin ya kare ga imamul hujja (A.F) .[1]

 Kumail Dan Ziyad Daya Daga Cikin Sahabban Amirul Muminin As, Ya Ruwaito Cewa: Amirul Muminin Ya Rike Hanuna Ya Fitar Da Ni Zuwa Ga Makabartar Jaban

Da a ka wayi gari sai yaja dogon numfashi sannan ya ce: bayan ya ambaci maganarsa mai tsayi har ya iso inda yake cewa : na rantse da Allah haka al’amarin yake, duniya ba ta zama ba tare da hujjar Allah ba, wanda zai tsaya wa Allah da hujjar sa ko dai wanda yake a fili a sarari sananne, ko wanda yake a boye a cikin tsoro,, don kada hujjojin Allah da dalilansa su rushe.[2]

 Ya zo cikin wata ruwaya mai bayani filla filla. daga haruna dan kharijah, ya ce: haruna dan sa’ad al’ijliy ya ce mini: ga shi isma’ilan da kuke mika wuya gare shi ya rasu, shi kuma Ja’afar ya tsufa, a gobe ko jibi zai rasu, sai ku zauna babu shugaba!! sai ban san irin amsar da zan fada masa ba, sai na labarta wa Abu Abdullahi (a.s) irin abin da ya fada sai ya ce: Allah ya kiyaye! Allah ya kiyaye! na rantse da Allah, Allah ba zai yarda wannan shugabancin ya yanke ba har sai dare da rana sun yanke.[3]

 Shekhus saduk ya ruwaito a cikin littafin kamalud din, ruwayar da take nuna cewa duniya ba za ta wanzu ba ba tare da hujjar Allah ba, har zuwa ranar tashin alkiyama.[4] kuma shi shekhus saduk ya yi sharhi sosai a kan wannan al’amarin, wanda za a iya dubawa don karin haske.

 


[1] Ash shekhus saduk, kamlud din, juzu’i na 1 babi na 22 shafi na 212 darul kutubul islamiyya kum, 1395 hijira kamariyya.

[2] Annu’umaniy, muhammd bin ibrahim, alghaibah, shafi na 136 maktabat assaduk Tehran 1397 hijira kamariyya.

[3] kamlud din juzu’i na 2 shafi na 657

[4] A duba kamalud din juzu’i na 1 babi na 22 shafi na 212

 

TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

  • menene hakikanin ma’anar salla?
    36439 Halayen Aiki 2012/07/25
    Salla daukakace ga duk mai san daukaka, ita ce hanya kai tsaye ba tare da shamaki ba, domin ita ce ganawa da ubangiji. Kamar yadda ya zo a Kur'ani mai girma cewa “hakika ni ne ALLAH wanda ba wani ALLAH sai ni to ku bauta ...
  • mece ce alakar jagorancin malami da jam'iyyu?
    7110 Tsare-tsare 2012/07/24
    Kungiyoyin siyasa, da ma'anar wasu jam'iyyu masu iri-iri akwai su a cikin kowace al'umma tun zamanin da. A yanzu ana ganin jam'iyyun siyasa a matsayin wani abu na tarayyar mutane da 'yancin zabe ne. bisa wannan asasin ne ya zama dole mu kalli wannan lamari a matsayin ...
  • Shin zai yiwu ai mana bayanin tafsirin suratu kausar?
    15332 Tafsiri 2017/06/17
    Suratu kausar sura ce da take da ayoyi guda uku, abin da ya fi shahara gun malamai shi ne an sauke ta a garin makka; sannan dalilin saukar ta shi ne yayewa manzon rahama (s.a.w) damuwar da yake ciki sakamakon mauta da gorin da wasu cikin kuraishawa ...
  • Ta yaya za a magance matsala, idan lamarin na hankali ya ci karon da na addini?
    14504 Sabon Kalam 2012/09/16
    Hankali shi ne hujjar Allah ta addini wacce ya ba wa mutum, hankali ke yi wa mutum jagora har ya kai shi ga samun cikakkiyar kamala, Shari`a hujja ce ta fili wacce take hana mutum gurbata da cutaya kuma ta kai shi ga samun cika da rabauta. ...
  • shin Imamul hujja a tsibirin bamuda yake zaune?
    15739 تاريخ بزرگان 2012/07/25
    Dalilin da ya sa wasu mutane suka yi ammanar cewa “Tsibirin Bamuda shi ne mazaunar Imamu Mahdi (a.s), gani suke Tsibirin Bamuda shi ne “Jazijrayul Khadra’a”. Bisa kaddara cewa Jaziratuk Khadra’a ita ce mazaunar Imamu Mahdi (a.s) shi ya sa suka ce Tsibirin Bamuda ya kunshi wadannan ...
  • Yaya aka samu sauyi a addinin Kiristanci, kuma da wane dalili ne ya samu karkacewa da jirkicewa
    12699 Sabon Kalam 2012/07/23
    Yayin da masu biyayya ga addinin Isa (a.s) suka haramata wa kawukansu wannan ni'ima ta samuwarsa a cikinsu, har ya samu hawa zuwa sama, sai manzanninsa da 'yan sakonsa suka ci gaba d aisar da sakonsa, kuma suka fuskanci wahalhalu masu yawa a kan hakan.
  • An lura da cewa Kur’ani mai girma shi ne mu’ujizar cika makin Manazannin Allah, to meye fuskokin gajiyarwar (kalu balen) da ke akwai a cikinsa?
    16211 Ilimin Kur'ani 2012/07/25
    An ambaci fuskokin gajiyarwar (kalu balen) da Kur’ani mai girma ya yi wadda zai yiwu na ambaci uku daga ciki: Ya gajiyar ta bangaren yare da bayani Ya gajiyar da fuskacin abin da ya kunsa Sannan kuma ya gajiyar ta ...
  • menene dalili a kan tabbatar shugabancin malami.
    18045 Hakoki da Hukuncin Shari'a 2012/07/26
    Akwai hanyoyi mabanbanta domin tabbatar da “shugabancin malami” sai dai a nan za mu isu da ambaton dalilai guda biyu na hankali da na ruwaya domin tabbatar da ita. Dalili na hankali: Hankali ya tabbatar da wajabcin samun mutumin da ke ...
  • Ta wace Hanya ake mangance maita da kanbun baka?
    40482 Halayen Aiki 2017/05/21
    Lalle Alkura'ani ma ya tabbatar da akwai maita, inda ya nuna wasu alamu da suke gaskata abin da tarihi ya tabbatar na daga cikin abin da Al’kur'anin ya zo da shi na daga al’umman da suka shude. Wasu malamai a wannan zamanin suna ganin wasu daga cikin ...
  • Menene hukunchi namijin da ba ya iya biyawa matarsa hakkokinta?
    13746 2019/06/16
    dawwamar rayuwar aure da karfafarta ya dogara da soyayya da kauna da fuskantar juna da girmama juna. Domin iyali su samu tsayuwa da dawwama Addini Muslunci ya sanya hakkoki ga kowanne dayansu ya kuma ayyana musu wajibai a kansu, duk sa”ilin da aka ce akwai hakkoki to ...

Mafi Dubawa