advanced Search
Dubawa
16400
Ranar Isar da Sako: 2012/04/04
Takaitacciyar Tambaya
Idan aka yi la’akari da ka’idar cewa duniya ba ta zama ba tare da hujjar Allah madaukaki a cikinta ba, shin wane ne hujja a tsakanin lokacin hawan saman annabi Isa (a.s) da lokacin tayar da annabi (s.a.w) ?
SWALI
Idan aka yi la’akari da ka’idar cewa duniya ba ta zama ba tare da hujjar Allah madaukaki a cikinta ba, wanda shi ne imami ma’asumi. Wannan shi ne abun da hujjar hankali ta tabbatar a cikin bincike game da akidar imamanci, shin wane ne hujja a tsakanin lokacin hawan saman annabi Isa (a.s) da lokacin tayar da annabi (s.a.w) ?
Amsa a Dunkule

Yana inganta a samu tazara a tsakanin annabawa masu shari”a, wato a aiko wani annabi kafin shekara dubu, sai wani annabin ya zo bayansa acikan shekara dubun, kuma wannan mas’alar ba ta warware hadisan da suke karfafa cewa ita duniya ba ta zama ba tare da hujjar Allah a cikinta ba, domin hujjar Allah da ake nufi ya shafi annabawa da imamai da halifofin annabawan.

 Hakika ya zo a cikin hadisai cewa duniya ba ta zama ba tare da hujjar Allah ba, wanda zai tsaya da hujjar Allah, ko dai wanda yake a fili a sarari sananne, ko wanda yake a boye a cikin tsoro, don kada hujjojin Allah da dalilansa su rushe.kuma ishara tazo a cikin hadisai a kan hujjojin Allah bayan annabi Isa (a.s) tun daga sham’un dan hamunis safa har ya kare da imamul hujja (A.T.F).

Amsa Dalla-dalla

Yana inganta a samu tazara a tsakanin annabawa masu shari’a, wato aiko wani annabi kafin shekara dubu, sai wani annabin ya zo bayan sa a cikan shekara dubun, kuma wannan mas’alar ba ta warware hadisan da suke karfafa cewa ita duniya ba ta zama ba tare da hujjar Allah a cikinta ba, sai dai ba ya inganta a ce kwata-kwata babu shi hujjar Allah din, a ce a duniya babu shi.

 A saboda haka a bisa lalura wajibi ne ya zamo akwai hujjar Allah a kowane lokaci da zamani don duniya ta iya wanzuwa da shi, ko dai wanda yake a fili a sarari sananne, ko wanda yake a boye a cikin tsoro”.

 Akwai wasu hadisai da suka yi nuni ga jerin sunayen halifofi da annabawa bayan annabi isa (a.s) har zuwa wannan lokacin namu, su ne: sham’un dan hamunissafa, shi kuma sham’un ya yi wasiyya ga yahaya dan zakariyya, shi kuma yahaya dan zakariyyaya ya yi wasiyya zuwa ga munzir, shi kuma munzir ya yi wasiyya zuwa ga sulaimat, shi kuma sulaimat ya yi wasiyya ga burdat, zuwa ga annabi (s.a.w) annabi ya yi wasiyya ga ali har wasiccin ya kare ga imamul hujja (A.F) .[1]

 Kumail Dan Ziyad Daya Daga Cikin Sahabban Amirul Muminin As, Ya Ruwaito Cewa: Amirul Muminin Ya Rike Hanuna Ya Fitar Da Ni Zuwa Ga Makabartar Jaban

Da a ka wayi gari sai yaja dogon numfashi sannan ya ce: bayan ya ambaci maganarsa mai tsayi har ya iso inda yake cewa : na rantse da Allah haka al’amarin yake, duniya ba ta zama ba tare da hujjar Allah ba, wanda zai tsaya wa Allah da hujjar sa ko dai wanda yake a fili a sarari sananne, ko wanda yake a boye a cikin tsoro,, don kada hujjojin Allah da dalilansa su rushe.[2]

 Ya zo cikin wata ruwaya mai bayani filla filla. daga haruna dan kharijah, ya ce: haruna dan sa’ad al’ijliy ya ce mini: ga shi isma’ilan da kuke mika wuya gare shi ya rasu, shi kuma Ja’afar ya tsufa, a gobe ko jibi zai rasu, sai ku zauna babu shugaba!! sai ban san irin amsar da zan fada masa ba, sai na labarta wa Abu Abdullahi (a.s) irin abin da ya fada sai ya ce: Allah ya kiyaye! Allah ya kiyaye! na rantse da Allah, Allah ba zai yarda wannan shugabancin ya yanke ba har sai dare da rana sun yanke.[3]

 Shekhus saduk ya ruwaito a cikin littafin kamalud din, ruwayar da take nuna cewa duniya ba za ta wanzu ba ba tare da hujjar Allah ba, har zuwa ranar tashin alkiyama.[4] kuma shi shekhus saduk ya yi sharhi sosai a kan wannan al’amarin, wanda za a iya dubawa don karin haske.

 


[1] Ash shekhus saduk, kamlud din, juzu’i na 1 babi na 22 shafi na 212 darul kutubul islamiyya kum, 1395 hijira kamariyya.

[2] Annu’umaniy, muhammd bin ibrahim, alghaibah, shafi na 136 maktabat assaduk Tehran 1397 hijira kamariyya.

[3] kamlud din juzu’i na 2 shafi na 657

[4] A duba kamalud din juzu’i na 1 babi na 22 shafi na 212

 

TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

  • Da”awar shi”a kan riddar sahabban mazon Allah {s.a.aw} bayan wafatinsa da wacce ma”ana sahabban su ka yi riddar? Shin wannan da”awa za ta iya karbuwa kuwa?.
    12161 Tsohon Kalam 2014/01/27
    samuwar karkata daga nau”in bidi”a da ridda tsakankanin sashen sahabban manzon Allah {s.a.w} bayan wafatinsa. Na farko: daga mahangar littafai na tushe na al”ummar musulmi faruwar hakan wani abu ne da aka sallamawa da babu kokwanto ko shakka ciki sannan kuma sam bai kebantu da littafan shi”a ...
  • Mene ne ma'anar jagorancin malami?
    12834 Sabon Kalam 2012/07/24
    Kalmar Wali da larabci tana da ma'ana guda uku: 1-masoyi, 2-aboki, 3-mataimaki. Bayan haka akwai wasu kalmomi kuma da suke nufin; 1-Salladuwa 2-Jagoranci da shugabanci. "Wilaya" kalma ce da ake amfani da ita da ma'ana biyu a isdilahin fikihu: 1- Wuraren da wanda ...
  • Shin mutum zai iya dawwama; idan haka ne, don me ya sa bai dawwama ba a duniya?
    11634 Sabon Kalam 2012/07/24
    Yana daga abin da yake jan hankli mai kyau a cikin kur’ani mai girma cewa yana ganin mutum wani halitta ne na sama madaukaki mai ‘yanci, kuma wannan jikin nasa ba komai ba ne sai wata sheka ta dan wani lokaci da ruhinsa ya fake a ciki ...
  • Menene hukuncin miji da mata wadanda suke kallon fim din blue fim a tare?
    6979 2018/11/04
    an tambayi daftrorin marja’ai masu alfarma kan tambayar da ka yi kuma ga amsar da suka turo. Ofishin mai girma Ayatullah sayyid Ali Khamna’i (Allah ya tsawaita rayuwarsa): Kalllon finafinai masu tada sha’awa na sa mutun ya karkata zuwa tafarkin shedan na son zuciya kuma yana raunana ...
  • WADAN NE BAITOCI NE ABBAS YAKE RERAWA A LOKACIN DA YA ZO DIBAN RUWA?
    11564 Sirar Manya 2012/07/26
    Mayaka yayin mubaraza a zamanin da su kan yi amfani da wani zaurance (don shaida juna ko ba da sako a tsakaninsu) don haka su kan rera baitotocin waka don samar da karfin gwiwa ga mutanensu da raunana abokan gaba. Imam (a.s) da mutanensa sun yi amfani ...
  • don me ake kiran annabi Muhammad (s.a.w) amintacce?
    6189 تاريخ بزرگان 2019/06/12
    Amintacce shi ne kishiyan mayaudari, watau ana nufin mutumin da ba ya yaudarar jama’a, kuma kowa ya natsu da shi ya dogara da shi bisa kyawun dabi’unsa. Idan muka waiga zuwa ga halayen Annabi (s.a.w) ta mu’amala da daidaku da al’umma tun a samartakarsa, zamu ga amana ...
  • Menene hukunchi namijin da ba ya iya biyawa matarsa hakkokinta?
    14051 2019/06/16
    dawwamar rayuwar aure da karfafarta ya dogara da soyayya da kauna da fuskantar juna da girmama juna. Domin iyali su samu tsayuwa da dawwama Addini Muslunci ya sanya hakkoki ga kowanne dayansu ya kuma ayyana musu wajibai a kansu, duk sa”ilin da aka ce akwai hakkoki to ...
  • Wasu irin hadisai ne suka zo a kan Hukuncin dan zina?
    14544 Dirayar Hadisi 2012/07/25
    Ruwayoyi na musulunci daga annabi (saw) sun yi magana da bayyana hukunce hukuncen dan zina, za mu kawo irin babobinsu Gadon dan zina;- Babin cewa dan zina, shi wanda ya yi zinar ba zai gaje shi ba, da ita mazinaciyar, ko wanda ...
  • Ta wace hanya za mu iya kare kanmu daga kanbun baka?
    26372 Tafsiri 2017/05/20
    Kanbun baka na da tasiri a ruhin mutun wanda babu wani dalili da za a iya kore samuwar sa da shi, ballantana ma an ga faruwar abubuwa masu yawa da suka tabbatar da samuwar kanbun baka ko maita. Marigayi shekh Abbas Kummi ya yi wasici da a ...
  • Shin zai iya yuwuwa a kai ga martabar ubangijintaka?
    8568 Irfanin Nazari 2012/07/25
    Makamin matsayin ubangijintaka yana da matakai da marhaloli mabambanta, kuma don a samu wannan amsar dole ne a ga dukkan martabobi da ma’anonin baki daya. Idan abin da ake nufi da kai wa matakin ubangijintaka shi ne zatin mutum ta canja da sauyawar abin halitta ya koma ...

Mafi Dubawa