advanced Search
Dubawa
14990
Ranar Isar da Sako: 2006/06/03
Takaitacciyar Tambaya
Mene ne ma’anar shirin Ubangiji wato (makru) a cikin Kur’ani mai girma?
SWALI
Mene ne ma’anar shirin Ubangiji wato (makru) a cikin Kur’ani mai girma?
Amsa a Dunkule

(Almakru) Yana zuwa da ma’anar shirya wani abu da kuma neman wani abu wanda yake shiga cikin ayyukan alheri da na sharri saboda haka ne aka yi amfani da ita a cikin Kur’ani mai girma abar jinginawa da siffa mummuna wato makirci.

Tanadin Ubangiji: Da akwai ayoyi masu yawa wadanda suke jingina tanadi zuwa ga Allah Madaukaki ita tana yin duba ne zuwa jujjuyawa gamammiya ga Allah Madaukaki domin cewa shi ne mamallakin jujjuyawa ba a samun wani abu da aka juya wanda ya fita daga kewayen jujjuyawarsu mai fadi saboda haka ne Allah Madaukaki ya kasance a saman dukkan wani mai shirya al’amura (Allah shi ne mafi alherin masu shiyar al’amura) Allah Madaukaki yana cewa:

﴿وقد مكر الذين من قبلهم فلله المكر جميعا يعلم ما تكسب كل نفس وسيعلم الكفار لمن عقبى الدار﴾

Ma’anar wannan aya shi ne: “Hakika wadanda suka gabace ku sun yi shirya al’amura to Ubangiji shi yake da shiri gaba daya, ya san abin da kowacce rai take aikatawa da sannu kafirai za su san wane ne yake da karshen makoma”.

Wannan ayar tana yi bayani karara a kan cewa jujjuya al’amari na gaba daya, yana ga Allah Madaukaki kuma jujjuya al’amuran wasu wanda yake fuskantar nasa ba shi da wata alama da za a ambata.

Amsa Dalla-dalla

Abin da ake nufi da (makru) ita kalmar makru a harshen Larabci tana zuwa da ma’anar jujjuyawa, wannan kuwa ya hade ma’anar tana nufin abu ne kyau ko kuma mara kyau,[1] wannan jujjuyawar ta kasance a cikin mummunan aiki ko kuma kyakkyawa tare da cewa wasu daga cikin malamai sun fasasra kalmar da ma’anar yaudara, amma yayin da ake jingina ta ga Ubangiji nan kuma tana zuwa da ma’anar sakamako da kuma ukuba.

TANADIN UBANGIJI:

Yayin da muke la’akari da ayoyin da aka yi amfani da kalmar (makru) a cikinta za mu ga cewa abin da ake nufi da (makru) shi ne jujjya al’amura da kuma bincike shig ada wand ake fita wani lokacin yana kasancewa a cikin al’amuran alheri wani lokacin kuma yana jawo ma’anar cuta.[2] Misalin wannan abin da ya zo a cikin aya mai girma a cikin fadinsa Madaukaki:

﴿ويمكرون ويمكر الله والله خير الماكرين﴾[3]

Ma’anar wannan aya shi ne: “Suna shirya makirci, Allah kuma yana yi musu shiri, Allah shi ne mafi alherin masu tanadi”[4].

Abin nufi da fadinsa: “suna shirya makirci” yaudara da abin da mushirikai suka kukkulawa na tanade tanade don su dauki fansa a kan Manzon Allah tsira da amincin Allah su kara tabbata a gare shi kamar shirin da suka yi don su kashe shi ko kuma su sanya shi a cikin kurkuku da makamancin hakan, amma abin nufi a cikin fadinsa: “Allah yana yin nasa shirin” shi ne shirin Allah mai girma da bwaya madauakakin sarki kamar umartarsa da ya yi da yin hijira ga misali.

A yayin da muke samun kalamr “makru” a cikin Kur’ani mai girma a inda ake siffanta ta da mummunan abu[5] wannan yana nufin cewa kalmar a wani lokacin tana kasancewa fuskantar sharri da mummunan abu a wani lokaci kuma da ma’anar fuskantar alheri da kyakkyawan wani abu a bisa wannan tushe ne cewa ayoyi masu yawa wadanda suke danganta (makru) zuwa ga Allah Madaukaki tana duba ne zuwa shirinsa gamamme kuma shi ne mamallaki, kuma mai kewaye da dukkan wani shiri da zai taba yiwuwa   ba a samu wani shiri ya fita daga kewayen jujjuyawarsa ta allantaka awcce take mai fadi gamammiya da wannan hasashe ne cewa Allah Madaukaki yake a saman dukkan wani mai kintsa shiri.[6] Hakika aya madaukakiya wacce take cikin suratur Ra’adi[7] tan ashiryarwa a zahirance da kuma bayanai a kan cewa jujjuyawa gamammiya tana kewaye ga Allah shi kadai kuma shirin wadansu ba komai ba ne idan aka danganta shi da shirin Allah Madaukaki ba zai yiwu ya tuke zuwa wani abu ba ma’abocin hankali.[8]

 


[1] Karshi sayyid aliyu akbar, kamusul kur’an j – 6 shafi 265.

[2] Almunjid madatuk makaru.

[3] A’arafi 99 da 123: fadir 10 da 43 ra’adu 33 da 42 saba’i 33 yunus 21 ali-imrana, 54 nahal 26 da 45 da namli 50 da 51, nahu 22, ibrahim 46 – yusuf 13 gafir 45.

[4] Anfal 30.

[5] Fadir 43.

[6] Ali Imrana, 54

[7] Ra’adu

[8] Allama taba-taba’i almizan tarjamar almusawi alhamdani. j – 12 shafi 20, 355, mujalladi, nashir, al-intisharat islamiyya.

 

TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

  • menene hakikanin ma’anar salla?
    36439 Halayen Aiki 2012/07/25
    Salla daukakace ga duk mai san daukaka, ita ce hanya kai tsaye ba tare da shamaki ba, domin ita ce ganawa da ubangiji. Kamar yadda ya zo a Kur'ani mai girma cewa “hakika ni ne ALLAH wanda ba wani ALLAH sai ni to ku bauta ...
  • mece ce alakar jagorancin malami da jam'iyyu?
    7110 Tsare-tsare 2012/07/24
    Kungiyoyin siyasa, da ma'anar wasu jam'iyyu masu iri-iri akwai su a cikin kowace al'umma tun zamanin da. A yanzu ana ganin jam'iyyun siyasa a matsayin wani abu na tarayyar mutane da 'yancin zabe ne. bisa wannan asasin ne ya zama dole mu kalli wannan lamari a matsayin ...
  • Shin zai yiwu ai mana bayanin tafsirin suratu kausar?
    15332 Tafsiri 2017/06/17
    Suratu kausar sura ce da take da ayoyi guda uku, abin da ya fi shahara gun malamai shi ne an sauke ta a garin makka; sannan dalilin saukar ta shi ne yayewa manzon rahama (s.a.w) damuwar da yake ciki sakamakon mauta da gorin da wasu cikin kuraishawa ...
  • Ta yaya za a magance matsala, idan lamarin na hankali ya ci karon da na addini?
    14504 Sabon Kalam 2012/09/16
    Hankali shi ne hujjar Allah ta addini wacce ya ba wa mutum, hankali ke yi wa mutum jagora har ya kai shi ga samun cikakkiyar kamala, Shari`a hujja ce ta fili wacce take hana mutum gurbata da cutaya kuma ta kai shi ga samun cika da rabauta. ...
  • shin Imamul hujja a tsibirin bamuda yake zaune?
    15739 تاريخ بزرگان 2012/07/25
    Dalilin da ya sa wasu mutane suka yi ammanar cewa “Tsibirin Bamuda shi ne mazaunar Imamu Mahdi (a.s), gani suke Tsibirin Bamuda shi ne “Jazijrayul Khadra’a”. Bisa kaddara cewa Jaziratuk Khadra’a ita ce mazaunar Imamu Mahdi (a.s) shi ya sa suka ce Tsibirin Bamuda ya kunshi wadannan ...
  • Yaya aka samu sauyi a addinin Kiristanci, kuma da wane dalili ne ya samu karkacewa da jirkicewa
    12699 Sabon Kalam 2012/07/23
    Yayin da masu biyayya ga addinin Isa (a.s) suka haramata wa kawukansu wannan ni'ima ta samuwarsa a cikinsu, har ya samu hawa zuwa sama, sai manzanninsa da 'yan sakonsa suka ci gaba d aisar da sakonsa, kuma suka fuskanci wahalhalu masu yawa a kan hakan.
  • An lura da cewa Kur’ani mai girma shi ne mu’ujizar cika makin Manazannin Allah, to meye fuskokin gajiyarwar (kalu balen) da ke akwai a cikinsa?
    16211 Ilimin Kur'ani 2012/07/25
    An ambaci fuskokin gajiyarwar (kalu balen) da Kur’ani mai girma ya yi wadda zai yiwu na ambaci uku daga ciki: Ya gajiyar ta bangaren yare da bayani Ya gajiyar da fuskacin abin da ya kunsa Sannan kuma ya gajiyar ta ...
  • menene dalili a kan tabbatar shugabancin malami.
    18045 Hakoki da Hukuncin Shari'a 2012/07/26
    Akwai hanyoyi mabanbanta domin tabbatar da “shugabancin malami” sai dai a nan za mu isu da ambaton dalilai guda biyu na hankali da na ruwaya domin tabbatar da ita. Dalili na hankali: Hankali ya tabbatar da wajabcin samun mutumin da ke ...
  • Ta wace Hanya ake mangance maita da kanbun baka?
    40482 Halayen Aiki 2017/05/21
    Lalle Alkura'ani ma ya tabbatar da akwai maita, inda ya nuna wasu alamu da suke gaskata abin da tarihi ya tabbatar na daga cikin abin da Al’kur'anin ya zo da shi na daga al’umman da suka shude. Wasu malamai a wannan zamanin suna ganin wasu daga cikin ...
  • Menene hukunchi namijin da ba ya iya biyawa matarsa hakkokinta?
    13746 2019/06/16
    dawwamar rayuwar aure da karfafarta ya dogara da soyayya da kauna da fuskantar juna da girmama juna. Domin iyali su samu tsayuwa da dawwama Addini Muslunci ya sanya hakkoki ga kowanne dayansu ya kuma ayyana musu wajibai a kansu, duk sa”ilin da aka ce akwai hakkoki to ...

Mafi Dubawa