advanced Search
Dubawa
8640
Ranar Isar da Sako: 2008/09/22
Takaitacciyar Tambaya
Shin a kwai wata madogara ta addini da ke nuna cewa turara kanyen esfand ko harmal na maganin riga kafi daga sharrin hassada?
SWALI
Shin akwai wata madogara a addini data nuna a Kona tsiron Harmal ko esfand don tsare kai daga Hassada?
Amsa a Dunkule
Ba zai yiwu ba ilimin da hankalin Dan Adam su riski wasu tabbatattun abubuwa ba, hassada ma na cikin waDancan abubuwan da hankali da ilimi basa iya tabbatarwa alal aKalla, hakama kuma hankali da ilimi basu samu dalilin kare hakan da watsi da shi ba.
Idan muka dawo kan nassoshin addini na Kur’ani da hadisai zai yiwu mu samu hujjojin da zasu tabbatar da haka.
Tabbas ayaKinance ilimi da hankalin mutum duk da har yanzu ba a kai ga gano haKiKanin hassada ba, tabbas ba zai yiwu a samo maganin hassada ba, to ashe fa lallai maganin hassada wajibi ne mu nemi taimakon nassoshin addani.
Ba a faDi wani maganin hassada da ake sha ba a cikin koyarwar addanin musulunci ba, don haka ba wata madogara a addinnance da tace ayi amfani da tsiron Harmal don kawar da hassada, duk da cewa an ambaci Harmal a matsayin maganin wasu cututtuka dake damun Ruhi da jiki. Tabbas Umarni da ambaton Allah da wasu keBantattun addu’o’i don samun kariya daga hassada haka ma ya zo a Daya daga cikin ruwayoyin cewa asalin Harmal Nushra ce (wato a matsayin ruKiyya yake).
 
Amsa Dalla-dalla
Ba shakka tabbas mutane suna gogayya da tabbatattun abuwa da abubuwan bogi waDanda suka sa musu tufafi mai kama da na gaske. Gafalallen mutum yana KoKarin kaiwa ga tabbataccen abu, ya kuma rayu akan tushen tabbas, sannan ya nisancewa abubuwan da basu da tabbas gwargwadon iko, duk da cewa abune mai wahala matuKa. Tabbas wasu abubuwa tabbatattu ana zaton Kanzon kurege ne, wasu abubuwan Kanzon kurege mutane na Daukan su gaskiya ne tabbatattu.
Wasu abubuwan an cakuDa su da Kanzon kurege da gaskiya don haka ana buKatar tankaDewa da rairaya A cikin irin waDan nan abubuwan dake cikin saKafar mutane da maganganun da ake yaDawa wanda suma sun cakuDa da Karerayi, akwai hassada wacce take iya cutar da wani sanadiyyar mahassadi in ya kalli wanda ya kewa hassada ba tareda ya yi wani aiki ba. Tasirin hassada baya aiki sai mahassadi ya kalli mutum ya Kayatu da niimar da yagani ta wanda yake yiwa hassada.
Tabbas musulunci da nazarinsa a wannan fagen yana amfanarwa tareda kawar da matsalar.
Hassada A Nazarin Kur’ani:
Malaman Tafsiri dayawa sun alaKanta waDannan ayoyin nan biyu da hassada:
1 -  Suratu Yusuf  ayata 47: A wannan ayar Allah na cewa: “Ya ‘ya’yana karku shiga ta Kofa Daya, ku shiga ta Kofufi daban-daban bazan kare muku wani abu ba daga Allah ba, hukunci sai ga Allah, gareshi na dogara don haka muminai su dogara gareshi”([1]).
Daya cikin abubuwan da aka faDa kan tafsirin wannan ayar shi ne hassada saboda ‘yan uwan Annabi Yusuf (a.s) suna da kyakkyawan kamanni da kyan sura, gashi kuma suna da yawa, sai Annabi Ya’aKuba (a.s) yaji tsoron kar mutanen Misra suyi musu hassada, don haka ya yi musu wasicci karsu shiga ta Kofa Daya kawai, su rarrabu, su shiga ta Kofofi da yawa don kar ayi musu hassada([2]).
2-  Suratu Kalam ayata 51: wannan ayar ta shahara a cikin saKafar mutane da ayar (wa in ya kadul lazina) itace mafakarsu don kariya daga hassada, acikin wannan ayar Allah na cewa: “Tabbas kafirai suna cewa lallai mahaukaci ne”([3]).
Allama DabaDaba’i ya faDa a Tafsirinsa: Abin nufi da sawa ya faDida idanuwansu shi ne kambun baka, akan wannan ne baki Dayan malaman Tafsiri suke, wani irin tasirin nafsu ne wanda ba za a iya kore shiba a hankalce, sau da yawa anga irin haka, sannan ruwayoyi sun zo a kan haka, don haka ba zancen inkarin hakan”([4]).
Tabbas yazo a cikin Tafsirin wannan ayar cewa ta sauka ne saboda tasiri da cutarwar kallon abu idan Banu Asad suka kalli abu, mutum a cikinsu yakanKi cin abinci har kwana uku, ba zai wuce ta kusa da abu ba ya ce “BantaBa ganin irinsa ba yau” face sai ya cutar da abin ba, sai wasu kafirai suka nemi wani mai irin haka don ya yiwa Annabi (s.a.w) irin haka, sai Allah yak are shi([5]).
Hassada A Cikin  Ruwayoyi:
Ruwayoyin da suka zo kan hassada suna da yawa, zai yiwu a kasa su kasha biyu:
  1. Ruwayoyin da suka zo kan tabbatar da cewa akwai hassada: Manzon Allah (s.a.w) yana cewa: “Tabbas kambun baka akwai shi yana iya faDo da dogon dutse”([6]).
Wannan ruwayar duk da tana Karfafa cewa hassada akwai ta tana kuma yin muni a kinayance kan tsananin tasirinta. A cikin waDannan ruwayoyin masu yawa bugu da Kari ga zuwan Karfafa kasancewar hassada tabbas ce anyi nuni a cikinsu kan tsananin tasirinta kuma.
Manzon Allah (s.a.w) ya faDa a wani hadisi “Tabbas kambun baka yana shigar da mutum kabari, yana kuma shigar da RaKumi tukunya”([7]).
Sirar Annabi (s.a.w) tana nuna cewa Amnzon Allah (s.a.w) ya yadda akwai tasirin hassada ya kuma faDi yadda za a warwareta, ya kuma yi amfani da hanyoyin warwareta. Tabbas an ruwaito Imam Hasan da Imam Husain (a.s) sunyi rashin lafiya saboda tasirin hassada sai Annabi (s.a.w) ya yi musu hirzi ya kuma yi musu addu’a keBantacciya wacce Jibrilu (a.s) ya sanar dashi don su warke([8]).
2-Ruwayoyin da suka ambaci yadda za ayi maganin hassada, a cikin ruwayoyin ba a faDi yadda za ayi maganin hassada ta hanyar shan magani ba don kawar da hassadada kare kai daga sharrin hassada, kawai dai anyi ishara a cikin da ambaton Allah cewa shi ne zai taimaka acikin haka inda Manzon Allah (s.a.w) yake cewa: kambun baka gaskiya ne duk wanda wani abun Dan uwansa ya Kayatar dashi to ya ambaci sunan Allah saboda in ya ambaci sunan Allah to ba zai cutar da shi ba([9]).
A wani hadisin Imam Ja’afar AsadiK (a.s) lokacin yana yin wasiyyar samun aminci daga hassada, ga abinda ya ce a faDa sau uku: “Masha Allah La Kuwwata illah billahil Aliyul Azim”([10]).
Manzon Allah (s.a.w) ya kasance yana amfani da wannan hirzin da Jibrilu ya koya masa lokacin yiwa Hasan da Husain (a.s) magani. Lokacin da suka yi rashin lafiya sanadiyyar hassada: Allahumma ya zazsulDanul Azim wal mannil Kadim wal wajhul karim zul kalimatit Tamat wadda’watil mustahabbat a’fil Hasani wal Husain min anfusil Jinni wa a’ayunin Nasi([11]).
Tabbas wasu hadisai sunyi wasiyyar a dinga cewa (Tabara kallahu ahsanul kaliKin, Allahumma barik fihi) sai a karanta Fatiha da Kulhuwallahu da Nasi da ayatul kursiyyu([12]).
Harmal da Hassada
Harmal tsiro ne da yake fitowa a wurare masu sahara kuma yana lissafa shi cikin tsirrai masu daDi: Tun  a da can ana amfani da shi wajen magunguna([13]).
Tabbas an ruwaito a cikin hadisai cewa a dinga amfani da Harmal don maganin wasu cututtukan Ruhi dana jiki, sai dai bai zo da wata kaifiyyar yadda za  a yi amfani da shi don yinmaganin hassada ba. Ruwayoyin da aka naKalto kan amfani da Harmal sun nuna shi a matsayin magani, kuma yana magance wasu cututtukan Ruhi kamar tsoro([14]).
Kamar haka aka faDa acikin ruwayoyi cewa yana amfani wajen maganin cututtukan jiki kamar Kurzunu([15]). Da Digar fitsari([16]).
Tabbas yazo a cikin ruwayoyi cewa asalin Harmal a matsayin ruKiyyar sihiri yake kamar yadda yazo a cikin ruwayar da aka karBo daga Amirul Muminina (a.s) kan asalin Harmal ruKiyya ne reshensa[17] kuma maganin cuta saba’in da biyu yake yi([18]).  Sai dai ruwayar ba ingantacciya ba ce a Bangaren sanadi ba.
Natija dai itace ba wata ruwayar dake nuna Harmal yana da tasiri kan karya ko maganin cututtukan jiki nan take.
 

[1] Suratu Yusuf aya ta 47.
[2] Dabrasi, alfadhlu bin Hasan  Majma’ul bayan fi tafsiril Kuran, J.3, sh 248 daru ihya’it turasil arabi, bairut 1379.
[3] Suratu Kalam 51.
[4] AlDaba’Daba’I Muhammad  Husain, Almizan J.20 sh 50. Bugu n BIYr Drul kurubul islamiyya. Taeran 1372.
[5] Alkashani fathullah, a cikn Manhaj Sadikin Fil izamil Mukhalifin J.9 sh 390, bugu na biyu, maktabatul islamiyya, Tehran 1344.  Da kuma alKummi, abbas, a cikin safinatul Bihar J. 6 sh 590. Bugu na biyu darul uswah iran 1416.
[6] Al sharif ridhawa a cikin Majazatul Nabawiyya sh 367. Manshurati maktabatu basirati, Kum. Ba tarihin bugawa.
[7] Almajidi gulamu Husain a nahajul fasaha j 2 sh 704, Bugu na daya mu’assasar ansariyan Kom, 1379. Da kuma Muhammad  BaKir  majlisi   Baharul anwar j 2 sh 39, bugu na farko mu’assasar wafa, beruit lubnon.
[8] Biharul Anwar J.92 sh 132, da J.60 sh 18.
[9] Bihar Anwar J.60 sh 25.
[10] Nahjul Fasaha J.2 sh 701,  Sunanul kubra Nasa’I J.6 sh 206. Bbuguna daya darul kutubul ilmiyya bairut 1411.
[11] Bihar J.9 sh 132.
[12] Bihar J.60 sh 25.
[13] Duba markaz Da’iratul Ma’arifil islamiyya Alkubra.
[14] Bihar J. 59 sh 234.
[15] Bihar J.59 sh 234.
[16] Bihar J.59 sh 188, Mustadrak wasa’il J.16 sh 446.
[17] Ma’ana nisantar da kai daga hassada.
[18] Alkufi, Muhammad  Dan Muhammad  alja’afariyyat, shafi 244. Maktabatu sabuwar ninawi, Tehran, a;tamimi almagribi, alnu’uman Dan Muhammad  a cikin da’aimul islam j 2 sh 150, darul ma’arif, misra.1385. da mustadrakul wasa’il j 16 sh 460.
TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

  • menene hakikanin ma’anar salla?
    36439 Halayen Aiki 2012/07/25
    Salla daukakace ga duk mai san daukaka, ita ce hanya kai tsaye ba tare da shamaki ba, domin ita ce ganawa da ubangiji. Kamar yadda ya zo a Kur'ani mai girma cewa “hakika ni ne ALLAH wanda ba wani ALLAH sai ni to ku bauta ...
  • mece ce alakar jagorancin malami da jam'iyyu?
    7110 Tsare-tsare 2012/07/24
    Kungiyoyin siyasa, da ma'anar wasu jam'iyyu masu iri-iri akwai su a cikin kowace al'umma tun zamanin da. A yanzu ana ganin jam'iyyun siyasa a matsayin wani abu na tarayyar mutane da 'yancin zabe ne. bisa wannan asasin ne ya zama dole mu kalli wannan lamari a matsayin ...
  • Shin zai yiwu ai mana bayanin tafsirin suratu kausar?
    15332 Tafsiri 2017/06/17
    Suratu kausar sura ce da take da ayoyi guda uku, abin da ya fi shahara gun malamai shi ne an sauke ta a garin makka; sannan dalilin saukar ta shi ne yayewa manzon rahama (s.a.w) damuwar da yake ciki sakamakon mauta da gorin da wasu cikin kuraishawa ...
  • Ta yaya za a magance matsala, idan lamarin na hankali ya ci karon da na addini?
    14504 Sabon Kalam 2012/09/16
    Hankali shi ne hujjar Allah ta addini wacce ya ba wa mutum, hankali ke yi wa mutum jagora har ya kai shi ga samun cikakkiyar kamala, Shari`a hujja ce ta fili wacce take hana mutum gurbata da cutaya kuma ta kai shi ga samun cika da rabauta. ...
  • shin Imamul hujja a tsibirin bamuda yake zaune?
    15739 تاريخ بزرگان 2012/07/25
    Dalilin da ya sa wasu mutane suka yi ammanar cewa “Tsibirin Bamuda shi ne mazaunar Imamu Mahdi (a.s), gani suke Tsibirin Bamuda shi ne “Jazijrayul Khadra’a”. Bisa kaddara cewa Jaziratuk Khadra’a ita ce mazaunar Imamu Mahdi (a.s) shi ya sa suka ce Tsibirin Bamuda ya kunshi wadannan ...
  • Yaya aka samu sauyi a addinin Kiristanci, kuma da wane dalili ne ya samu karkacewa da jirkicewa
    12699 Sabon Kalam 2012/07/23
    Yayin da masu biyayya ga addinin Isa (a.s) suka haramata wa kawukansu wannan ni'ima ta samuwarsa a cikinsu, har ya samu hawa zuwa sama, sai manzanninsa da 'yan sakonsa suka ci gaba d aisar da sakonsa, kuma suka fuskanci wahalhalu masu yawa a kan hakan.
  • An lura da cewa Kur’ani mai girma shi ne mu’ujizar cika makin Manazannin Allah, to meye fuskokin gajiyarwar (kalu balen) da ke akwai a cikinsa?
    16211 Ilimin Kur'ani 2012/07/25
    An ambaci fuskokin gajiyarwar (kalu balen) da Kur’ani mai girma ya yi wadda zai yiwu na ambaci uku daga ciki: Ya gajiyar ta bangaren yare da bayani Ya gajiyar da fuskacin abin da ya kunsa Sannan kuma ya gajiyar ta ...
  • menene dalili a kan tabbatar shugabancin malami.
    18045 Hakoki da Hukuncin Shari'a 2012/07/26
    Akwai hanyoyi mabanbanta domin tabbatar da “shugabancin malami” sai dai a nan za mu isu da ambaton dalilai guda biyu na hankali da na ruwaya domin tabbatar da ita. Dalili na hankali: Hankali ya tabbatar da wajabcin samun mutumin da ke ...
  • Ta wace Hanya ake mangance maita da kanbun baka?
    40482 Halayen Aiki 2017/05/21
    Lalle Alkura'ani ma ya tabbatar da akwai maita, inda ya nuna wasu alamu da suke gaskata abin da tarihi ya tabbatar na daga cikin abin da Al’kur'anin ya zo da shi na daga al’umman da suka shude. Wasu malamai a wannan zamanin suna ganin wasu daga cikin ...
  • Menene hukunchi namijin da ba ya iya biyawa matarsa hakkokinta?
    13746 2019/06/16
    dawwamar rayuwar aure da karfafarta ya dogara da soyayya da kauna da fuskantar juna da girmama juna. Domin iyali su samu tsayuwa da dawwama Addini Muslunci ya sanya hakkoki ga kowanne dayansu ya kuma ayyana musu wajibai a kansu, duk sa”ilin da aka ce akwai hakkoki to ...

Mafi Dubawa