advanced Search
Dubawa
6545
Ranar Isar da Sako: 2011/04/11
Takaitacciyar Tambaya
shin Allama Majlisi na daga cikin wadanda suka habaka Daular Safawiyawa, kana mai yaba wa mahukuntanta?
SWALI
Shin Allama Majlisi na daga cikin wadanda suka habaka daular safawiyawa kana mai yaba wa mahukuntanta?
Amsa a Dunkule

Dangantaka tsakanin malaman Shi’a da mahukuntan daular Safawiya da ma mahukunta na wasu dauloli da nufin raunana Shari’a ba ne. Dalilan yin hakan su ne samar da mamora da kyakkyawan manufa ga al’umma da yin wannan alakar kan haifar don taimakon jama’a da yada Mazhabar Shi’a da al’umma, kana akwai manufar yada ilimi da fahimtar Addini bisa dogara da cewa ikon fada aji da hukuma take da shi.

Daga cikin zarge-zargen da ake dangane da alkar Allama Majlisi ta siyasa har da zuwansa fada tare da tawagar mahuntan Safawiyawa da kuma taimakawa sarakuna na zamaninsa. Babu Shakka malami kan bada kai ga yanayi da suka samu kansu a ciki. Irin alakar Allama Majlisi ba ita ce farau a gun malamai ba. Tabbas irin wadannan malamai na Shi’a suna tafi da harkokinsu ne bisa tafarki na Imamai Ma’asumai  (a.s) wadda –wani lokaci- takan ginu bisa turbar amfani da sarakuna ‘yan-kama-karya da halifofi azzalumai ta hanyar duba na sanaki ga yanayin da ake ciki musamman a bagaren mahimman lamura da matsaloli da suka Shafi duniyar musulmi da zamantakewa da ilmatarwa, ta hanyar amfani da wannan alakar da nufin aiki tukuru don samar da fa’ida da nufin amfanar da al’umma da shiryar da mutane da samar da gyara a al’umma, musamman a gefen yada Addini da yada Mazhaba ta gaskiya da kokarin samar da adalci na rayuwa. To a nan zamu iya ganin dalilai da suka sa Allama Majlisi ya yi wannan hubbasar bisa wannan manufar, watau bai yi hakan don wata manufa tasa ta kashin kai ba. Wannan hubbasar tasa ta samu ne bisa yanayi da ya samu kai a ciki da nufin cimma wancan manufar da hadafi na siyasa. Ko da yake akwai malamai da suke da ra’ayi da ya saba nasa na katse duk wata alaka da mahukuntan Safawiyawa da ma wasunsu.

Amsa Dalla-dalla

Dangantaka tsakanin malaman Shi’a da mahukuntan daular Safawiya dama wasu mahukunta na wasu dauloli ba da nufin raunana Shari’a ba ne. Dalilan yin hakan su ne samar da alfanu da kyakkyawan manufa ga al’umma da yin wannan alakar kan haifar don taimakon jama’a da yada Mazhabar Shi’a da taimkon al’umma, kana akwai manufar yada ilimi da fahimtar Addini bisa dogara da cewa  ikon fada-aji da hukuma ke da shi. Kare malamai daga shiga hadari, samun damar  bayyana musa mutanen kirki don ba da kariya ga gurare masu albarka yayata hukunce-hukuncen Shari’a a tsakanin al’umma duk wannan kan samu ne ta hanyar kyautata alaka tsakanin malamai da sarakunan Safawiyawa. Bisa gaskiya manufarsu ba bishe Shari’a ba ne, manufa ce ta yada karantarwa da ilimi. Abin lura a nan shi ne wannan alakar da kyatata fahimtar juna wata dama ce a wani zamani ta sanin Ubangiji. Abin lura a nan shi ne wancan alakar da fahimtar juna wata mahimmiyar dama ce a tarihance kana gaba ce ta samun kyakkyawar dama ga Shi’a a wannan lokacin.

MaSharhanta game da daular Safawiyawa a wannan zamani sun yi amannar cewa “Tushen daular Safawiyawa ya faro ne a matsayin kungiya ta wannan hanyar ce daular ta samu shimfida ikonta da kafuwa da tabbatar dokokinta. Tsarinta na masarauta ya kunshi sassan bangaren soja, wadda kowane sashi na da nasa aikin, kana akwai bagaren tafiyar da mulki mai kare dokoki da tsara bukukuwa na Addini da ke karkashin malaman musulmi da yadawa da bunkasa harkokin Mazhabobi, karfafawa a kan batun wilaya da bara’a, da tsattsara bukukuwa na farin ciki da na takaici da idudduka na Addini da…, duk wadannan ababe sun yi matukar taka rawa wajen habaka siyasar Iraniyawa a daular Safawiyawa.”[1]

Dangantaka Tsakanin Allama Majlisa Da Mahukuntan Daular Safawiya

Daga cikin zarge-zargen da ake yi dangane da alakar Allama Majlisi ta siyasa har da zuwansa fada tare da tawagar mahukuntan Safawiyawa da kuma taimakawa sarakuna na zamaninsa. Kafin shiga wannan batun muna ganin ya zama tilas mu yi nuni zuwa ga wani muhimmin zance shi ne:   Hakika malaman Shi’a a karkashin daular Safawiyawa a zamanin sarki Sha kafin kafuwar daular Musulunci sun rayu ne a hali na takaici da shiga tasku da nisanta su a fagen siyasa da harkar zamantakewa ta yadda aka nisanta malaman Shi’a da wakilansu daga kowane irin mukami na harka da  jama’a. Wannan ke nan! A daya gefen su kuwa talakawa sun sallama wa wadannan mahukuntan. Tambaya a nan ita ce, wane mataki za’a dauka  idan aka tsinci kai cikin wannan yanayi? Shin ya dace a tunkari wannan hukumar ta hanyar fadanci da bambadanci da amfani da addini? Ko fito-na-fito da fafatawa da yanke hulda da rashin bada kai ga mahukunta?  Shin zai yi kokarin wayar da kan jama’a don kau da matsalar?  Ko ya wajaba ya shelanta jahidi don kau da ita da nufin kafa halattacciyar gwamnati da rusa ta baya? Ko kuma kyakkyawar mafita a irn wannan yanayi shi ne bude kofar tattaunawa da hada kai da mahukunta don samar da fa’ida da maslaha ga Addini da Mazhaba da ma al’umma?.

Babu Shakka malamai kan bada kai ga yanayi da suka samu kansu a ciki. Irin alakar Allama Majlisi ba ita ce farau a gun malamai ba. Tabbas irin wadannan malamai na Shi’a suna tafi da harkokinsu ne bisa tafarki na Imamai Ma’asumai  (a.s) wanda –wani lokaci- takan ginu bisa turbar amfani da sarakuna ‘yan kama-karya da halifofi azzalumai ta hanyar duba na tsanaki ga yanayin da ake ciki musamman a bagaren mahimman lamura da matsaloli da suka shafi duniyar musulmi da zamantakewa da ilmantarwa,  ta hanyar amfani da wannan alakar da nufin aiki tukuru don samar da fa’ida da nufin amfanar al’umma da shiryar da mutane da samar da gyara a al’umma, musamman a fagen yada Addini da yada Mazhabar  gaskiya da kokarin samar da adalci a cikin rayuwa. A irin wannan halin malaman Shi’a kan yi kokarin samar da kyakkyawar yanayi da nufin haifar da fa’ida ga jama’a ta hanyar wannan alakar. Wannan salon zamu gan shi a tsarin rayuwar Amirul muminina (a.s) haka kuma a rayuwa ta Imamai (a.s) na bayansa. Ga misalai:

- Taimakon da Amirul muminina (a.s) ya yi ga daulolin halifofin nan uku, da karbar mukamin gwamnan Ahawa’az da almajirin Imamu Sadik (a.s) watau Abdullahi Annajashi ya yi, Aliyyu bin Yakdin ya rike ministan kudi a gwamnatin Harunarrashid bisa umurnin Imamu  Kazim  (a.s), Imamu  Rida  (a.s) ya karbi makamin wilayatul ahad (yarima) a gwamnatin Ma’amun  Abbasi, Alkawaja Nasiruddin Dusi ya yi aiki a gwamnatin Holako da sauran su. Kazalika manyan malamai na Shi’a shigarsu gwamnatin Safawiyawa ya  taimaka a bangaren siyasa, malaman sun hada da gogaggen masani Alkarki, sheikh Baha’i, Allama Majlisi babba da Majlisi karami da sauran su, sun riki wasu mukamai na siyasa a fannin Addini. Abin lura a nan shi ne shigarsu gwamnatin Safawiyawa ba ya nufin sun shiga ne don bukata ta kashin kai ko samun matsayi ko mukami don tara dukiya ko kudi ba. Sun yi kokarin ne da nufin kare daula ta Shi’anci ta wani gefen. Wajabcin kulla wannan kyakkyawar alaka kan iya bayyana karara idan aka dubi wariya da a kan yi wa malaman Shi’a a tsawon tarihi. A bisa dabi’a kulla kyakkyawar alaka tsakanin mahukunta takan tsayu ne da nufin samar da wata dama ga malamai na sauke wani muhimmin nauyi da ke wuyansu da nufin kare Addini da Mazhaba da yada ta don ida sako na ilmantarwa da kare gundarin Mazhabar Shi’a da  kakkafa makarantun Hauza da ilimi da sauran su.

Domin karin bayani za’a iya duba gurare kamar haka:

  1. Marwi Baradanshiya siyasi Allama Majlisi; izalatu mazhab siyasi inda Allama Majlisi.
  2. Mujallat Hukuma Islamiya, daba’i na 20,suldan muhammadi, Abulfadal; <mururu bar’andake siyasia=Allama Muhammad Bakir Majlisi>

 


[1] . Nahram Nazad Muhusin safawiyah darkastara tarikh Iran zamin sh99, (makalar siyasar kan daujjlar Safawiyawa), daba’in IntiShara’at sanwidah,  jami’ar Tehran 1383 HK.

 

TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

  • menene hakikanin ma’anar salla?
    36439 Halayen Aiki 2012/07/25
    Salla daukakace ga duk mai san daukaka, ita ce hanya kai tsaye ba tare da shamaki ba, domin ita ce ganawa da ubangiji. Kamar yadda ya zo a Kur'ani mai girma cewa “hakika ni ne ALLAH wanda ba wani ALLAH sai ni to ku bauta ...
  • mece ce alakar jagorancin malami da jam'iyyu?
    7110 Tsare-tsare 2012/07/24
    Kungiyoyin siyasa, da ma'anar wasu jam'iyyu masu iri-iri akwai su a cikin kowace al'umma tun zamanin da. A yanzu ana ganin jam'iyyun siyasa a matsayin wani abu na tarayyar mutane da 'yancin zabe ne. bisa wannan asasin ne ya zama dole mu kalli wannan lamari a matsayin ...
  • Shin zai yiwu ai mana bayanin tafsirin suratu kausar?
    15332 Tafsiri 2017/06/17
    Suratu kausar sura ce da take da ayoyi guda uku, abin da ya fi shahara gun malamai shi ne an sauke ta a garin makka; sannan dalilin saukar ta shi ne yayewa manzon rahama (s.a.w) damuwar da yake ciki sakamakon mauta da gorin da wasu cikin kuraishawa ...
  • Ta yaya za a magance matsala, idan lamarin na hankali ya ci karon da na addini?
    14504 Sabon Kalam 2012/09/16
    Hankali shi ne hujjar Allah ta addini wacce ya ba wa mutum, hankali ke yi wa mutum jagora har ya kai shi ga samun cikakkiyar kamala, Shari`a hujja ce ta fili wacce take hana mutum gurbata da cutaya kuma ta kai shi ga samun cika da rabauta. ...
  • shin Imamul hujja a tsibirin bamuda yake zaune?
    15739 تاريخ بزرگان 2012/07/25
    Dalilin da ya sa wasu mutane suka yi ammanar cewa “Tsibirin Bamuda shi ne mazaunar Imamu Mahdi (a.s), gani suke Tsibirin Bamuda shi ne “Jazijrayul Khadra’a”. Bisa kaddara cewa Jaziratuk Khadra’a ita ce mazaunar Imamu Mahdi (a.s) shi ya sa suka ce Tsibirin Bamuda ya kunshi wadannan ...
  • Yaya aka samu sauyi a addinin Kiristanci, kuma da wane dalili ne ya samu karkacewa da jirkicewa
    12699 Sabon Kalam 2012/07/23
    Yayin da masu biyayya ga addinin Isa (a.s) suka haramata wa kawukansu wannan ni'ima ta samuwarsa a cikinsu, har ya samu hawa zuwa sama, sai manzanninsa da 'yan sakonsa suka ci gaba d aisar da sakonsa, kuma suka fuskanci wahalhalu masu yawa a kan hakan.
  • An lura da cewa Kur’ani mai girma shi ne mu’ujizar cika makin Manazannin Allah, to meye fuskokin gajiyarwar (kalu balen) da ke akwai a cikinsa?
    16211 Ilimin Kur'ani 2012/07/25
    An ambaci fuskokin gajiyarwar (kalu balen) da Kur’ani mai girma ya yi wadda zai yiwu na ambaci uku daga ciki: Ya gajiyar ta bangaren yare da bayani Ya gajiyar da fuskacin abin da ya kunsa Sannan kuma ya gajiyar ta ...
  • menene dalili a kan tabbatar shugabancin malami.
    18045 Hakoki da Hukuncin Shari'a 2012/07/26
    Akwai hanyoyi mabanbanta domin tabbatar da “shugabancin malami” sai dai a nan za mu isu da ambaton dalilai guda biyu na hankali da na ruwaya domin tabbatar da ita. Dalili na hankali: Hankali ya tabbatar da wajabcin samun mutumin da ke ...
  • Ta wace Hanya ake mangance maita da kanbun baka?
    40482 Halayen Aiki 2017/05/21
    Lalle Alkura'ani ma ya tabbatar da akwai maita, inda ya nuna wasu alamu da suke gaskata abin da tarihi ya tabbatar na daga cikin abin da Al’kur'anin ya zo da shi na daga al’umman da suka shude. Wasu malamai a wannan zamanin suna ganin wasu daga cikin ...
  • Menene hukunchi namijin da ba ya iya biyawa matarsa hakkokinta?
    13746 2019/06/16
    dawwamar rayuwar aure da karfafarta ya dogara da soyayya da kauna da fuskantar juna da girmama juna. Domin iyali su samu tsayuwa da dawwama Addini Muslunci ya sanya hakkoki ga kowanne dayansu ya kuma ayyana musu wajibai a kansu, duk sa”ilin da aka ce akwai hakkoki to ...

Mafi Dubawa