advanced Search
Dubawa
11709
Ranar Isar da Sako: 2010/01/19
Takaitacciyar Tambaya
WADAN NE BAITOCI NE ABBAS YAKE RERAWA A LOKACIN DA YA ZO DIBAN RUWA?
SWALI
SHIN YIN KABBARA SHI NE ALAMA (TA SADARWA) TSAKAKIN ABBAS DA RUNDUNAR (IMAM) KO KUMA A’A?
Amsa a Dunkule

Mayaka yayin mubaraza a zamanin da su kan yi amfani da wani zaurance (don shaida juna ko ba da sako a tsakaninsu) don haka su kan rera baitotocin waka don samar da karfin gwiwa ga mutanensu da raunana abokan gaba. Imam (a.s) da mutanensa sun yi amfani da take iri-iri da baitoci don ba da kwakkwarar hujja dake dauke da mahimman sakonni a ranar Ashura. Daga cikinsu akwai dan uwansa Abulfadal Abbas (a.s) da ya yi ta rera baitoci masu dadin gaske a lokuta daban-daban a ranar Ashura don zaburar jama’ar Imam Husaini (a.s) da kwantar da hankalinsu musamman yara da mata don tabbatar musu da cewa yana raye ba a kasheshi ba. Za mu kawo wasu daga cikinsu kamar haka:

Alokacin da yara suka riku daga murya da kuka saboda tsananin kishin ruwa, sai Imam Husaini (a.s) ya aiki dan uwansa Abbas ya debo ruwa a bakin kogi. Abbas ya tunkari dakaru 4000, masu tsaron ruwa don su hana shi diba, sai ya fuskancesu yana rera baitoci yana gunji kamar haka:

“Zan yaki mutanen da zuciya ta shiriya

Ina mai kare jikan Ahmadu (Annabi)

Ina saranku da tokobi mai kaifi

Har sai kun kauce wa yakar shugabana

Ni ne fa Abbas mai nuna kauna ga

Zuriyar Aliyu Murtala karfafaffe”.

Sai ya rika korar su gefen dama da hagu, ya kashe musu mutane masu yawa, yana gunji da baitoci:

“ba na shayin mutuwa idan mutur ta zo

Ko da zan gamu da wahala yayin gamuwar

ni Abbas na yi nufin shayar da ruwa

ba na shayin mutuwa a ranar gamo”

Bayan ya isa bakin ruwa sai ya kamfata da hanunsa ya debo don ya sha sai ya tuna kishin Imam Husaini (a.s) sai ya watsar da rowan ya na mai rera wake yana fadi:

“Ke rai bayan Husaini kin tozarta

A bayansa bai dace ki rayu ba

Ga can Husaini na tinkarar mutuwa

Amma zaki sha ruwa mai sanyi

To wallahi Addinina bai ce haka ba”

Sannan sai suka fara ruwan kibau da na masu a kansa, Zaidu ibin Warka ya lababo ya sare hanunsa na dama, (bai kareya ba) sai ya rike tokobinsa da hanunsa na hagu yana mai rera baitoci:

“Wallahi don kun yanke mun hanun damana

Har abada zan ci gaba da kare addinina

Zan kare Imamina na gaskiya bisa tabbas”

Tsatsaon Annabi Maitsarki Amitattace[1]

Wannan wani sashe ne daga cikin baitocin Abbas da kuma kirarinsa a ranar Ashura. Zance na cewa ya zabi yin kabbara a matsayin alama ta nuna yana raye a lokacin da ya je debo ruwa, bamu samu wata kafa da ke nuna wanna bayanin ba. Sai dai a kwai wasu alamomi na (na sadarwa) da nuna wani abu ya faru da suka danganci kabbar irinsu “Babu wata dabara babu wani karfi sai na Allah” Wannan na cikin fitattun alamomi na nuna faruwar abu a tsakanin rundunar Imam Husaini (a.s). Kasantuwar Ubaidullahi bin Ziyad da yan kanzaginsa irin su Umar bin Sa’ad da waninsa wai suna yakar Imam Husaini (a.s) ne da sunan Musulunci haka fafatawarsu da Kawarijawa, babu mamaki suma su yi ammfani da wannan taken.

 


[1].  A wasu daga cikin wake-waken Sayyid Abbas (a.s). a ranar Ashura.

 

TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

  • Meye matsayin jagorancin malami a tsarin siyasar musulunci?
    8086 کلیات 2012/07/24
    A zamanin boyuwar Imam Mahadi (a.s) "jagorancin malami" wani asasi ne tabbatacce kuma doka gama gari ta duniya wacce take daga tsarin siyasar musulunci, kuma matsayin malami dole ne ya kasance a matsayin jagora a matsayin shugaba mai yanke hukunci da bayar da umarni kuma ya kasance ...
  • Wadananne ne muhimman siffofin tafsirin Kur\'ani na wannan zamanin?
    6496 Ilimin Kur'ani 2019/06/16
    Tsarin tafsirin wannan zamani na da kebance - kebance da kuma da nagartar da babu ita a cikin tafsiran da suka gabata: ta bangaren amsa shibuhohi da warware tambayoyi da lamurran da suke kai- kaiwa a kasuwar tunani da kwakwalen mutane, bisa dogaro da tafarkin yin amfani da ...
  • mene ne ma’anar Takawa?
    17318 تقوی 2012/07/25
    Takawa wani karfi ne cikin ruhin mutum mai tsawatarwa da hana shi aikata ayyukan kuskure, kamalar takawa na kasancewa in an hada da nesantar abubuwan haramun, kamar nesantar shubha. Kuma ita Takawa tana da marhaloli da rabe-rabe, da kuma alamomi, zamu bijiro da su a jawabi na ...
  • mi ake nufi da makamta a ranar lahira?
    16001 معاد و قیامت 2012/11/21
    Abun nufi da makamta a cikin wannan ayar[i] da sauran ayoyi makamantanta[ii] ba shi ne rashin gani irin na duniya ba {wato mutun ya zamo bai gani da idanuwan da yake dasu} , sai dai abun nufi shi ne mutun da ...
  • Shin hadisin da ke cewa “duk wanda ya mutu ba shi da bai’ar imamin zamaninsa (Imaminsa) ya yi mutuwar jahiliyya” daga manzo (s.a.w) yake kuwa?
    9625 گوناگون 2012/07/26
    Bai’a na da bangarori biyu, mai bai’a (sauran mutane) da wanda ake yi wa bai’ar (wato su ne manzo (s.a.w) da imamai (a.s)). Tare da cewar manzo (s.a.w) shi ne hujja kuma shugaba, don haka shi za a yiw mubayi’a a matakin farko wato shi ne farkon ...
  • Shin mutum mai yawan tafiya zai yi kasaru kan hanyarsa ta tafiya ko dawowa wacce ba ta kai kwana goma ba?
    9278 2019/06/16
    Maraji”an takalid masu daraja, sun tafi kan cewa mutanen da tafiye tafiye ya kasance matsayin sana”a garesu to wajibi ne su cika sallah su kuma yi azumin ramadana halin tafiyar sai dai cewa game da adadi da gwargwadon tafiyar da za ta kasance da wannan hukunci na ...
  • mene ne gwargwadon tasirin Allah madaukaki a rayuwar mutum?
    16378 Irfanin Nazari 2012/07/25
    Ba yadda za a wani aiki ya fita daga iradar Allah mai hikima, wannan iradar ta Allah tana nan a ko da yaushe a rayuwar mutum a kowane lokaci da zamani, da dukkan dokokin rayuwa ba tare da ta cire wa mutum zabin da yake da shi ...
  • A zaben jagora malami ba kai tsaye ba akwai matsalar kai-kawo, to yaya za a warware wannan?
    7661 انتصاب یا انتخاب 2012/07/24
    A yanzu haka a jamhuriyyar musulunci ta Iran ana ayyana ‘yan takarar majalisar Khubrigan ta hannun shura Nigahban ne. To akwai batun sukan cewa Jagora shi ne yake ayyana ‘yan shura Nigahban, su kuma suke ayyanar cancantar shiga takara ga ‘yan majalisar khubrigan, su ‘yan majalisar khubrigan ...
  • yaya halittar mutum take a a mahangar musulunci?
    10480 Sabon Kalam 2012/07/23
    Ta mahangar Kur’ani mutum halitta ce da yake fizguwa zuwa ga ubangjinsa bisa fidirar halittarsa, kuma yake da jawuwa zuwa ga jiki, wannan halittar tana jansa zuwa ga ilimi da sani da alherai, a daya bangaren jiki tana kiransa zuwa ga sha’awa da sharri. Rayuwar mutum wani ...
  • Shin zan iya samun dama game da yin wani aikin na biyu bayan wanda nake yi
    7035 دنیا و زینتهای آن 2012/07/25
    Shari’a ba ta hana mutum yai koyi ko ya kware kan wata sana‘ar ba bayan wacce yake yi ko ya iya ko yin aiki sama da yadda ya saba abin kawai da shari’a ta hana kuma take kara tsoratarwa a kansa shi ne son duniya da nace ...

Mafi Dubawa