advanced Search
Dubawa
11542
Ranar Isar da Sako: 2007/11/17
Takaitacciyar Tambaya
Shin da wacce mahanga Kur’ani ke kallon mutum? a matsayin wanda yake yin zalunci da jahilci, ko kuma halifan Allah a bayan kasa?
SWALI
Shin da wane ido kur’ani ke kallon mutum? a matsayin wanda ke yin zalunci da jahilci, ko kuma halifan Allah a bayan kasa?
Amsa a Dunkule

1- Kur’ani ya yi nuni a wasu ayoyi cewa mutum na da matsayi madaukaki sai dai amma a wani bangaren da mafiya yawan ayoyi yana zarginsa da tare da yi masa gargadi

2-matsayin dan Adam dan Adam na da wani abin mai ban mamaki wajan kololuwar darajar da Allah tya yi masa da kuma wajan fadowarsa a daraja wanda tazarar daukakar da kaskancin ya fi nisan sama da kasa, saboda irin wannan abin mamakin da mutum ke da shi za ka samu yana da wasu abubuwan da suka sabawa al’ada.

3- mutum nag a bangare biyu na samuwa, bangaren ransa wato samuwarsa da bangaren jikinsa na zahiri.

4- mutum na da halayyar da ta sabawa sauran dukkan halittu domin anyishi da damar zabar hanyar da ya ga tafi dacewa da shi, tare da dabiantuwa da duk yanayin da ya smu kansa a ciki.

5- daga mutane ne a kan samu wadanda aka kira su a matsayin halifofin Allah a bayan kasa kuma suka cananci a kira su da wannan matsayi babba, wadannan su ne wadnda Allah ya shirye su da shiriyar sa domin sun yi nisa da dukkan abubuwan kyale kyalen rayuwa da kuma son ransu suka kuma sanya shi karkashin hukuncin mahaliccinsu wanda shi ne ya fi dacewa a wajan su.

Amsa Dalla-dalla

Idan muka yi la’akari da wasu ayoyi daga kur’ani,ai girma muna iya kaiwa ga natija kamar haka; mufara duba ayoyin da suke magana a kan daukakar sha’anin dan Adam da fifikonsa kan dukkan halittu tare da nuna abubuwan da ya kebanta da su kamar; “hakika mun girmama dan Adam kuma muk daga shi a cikin kasa da ruwa (teku) kuma muka azurtasu daga abubuwa masu dadi tsarkaka kuma muka fifita su a kan mafiya yawa daga cikin abababan halitta fifitawa”[1]             “a lokacin da ubangijinka ya ce da mala’iku babu shakka ni mai sanya halifa ne a bayan kasa”[2]             “lallai mun bijirar da amana ga sammai da kassai da duwatsu suka ki daukarta kuma suka ji tsoronta amma sai mutum ya dauka domin kuwa shi mai yawan zaluci ne kuma mai yawan jahilci”[3] da dauransu   wannan bangaren yabo ke nan.

 Bangarorin ayoyi na biyu kuwana zargi mutum tare da tsawatar masa daga ayyukann da ke kaskantar da zuciya kamar fadin Allah cewa “mutum na da yanke kauna da kasawa”[4] “da Allah ya shimfida arzikinsa ga bayinsa shimfidawa da sun yi zaluncin da rarraba kan jama’a a cikin kasa”[5]        “mai yawan zalunci ne kuma mai yawan kafirci”[6] “ya kasance mai yawan zaluntar kansa kuma mai jahilci”.[7] “mai yawan husuma ne tare da bayyana ta”.[8]  “lallai mutum na cikin tabewa (hasara)[9]     

A bisa assin wadannan ayoyin da suka gabata muke kara dora tambayarmu da cewa; menene sirrin hakan kuma me wadannan ayoyi da ke karo da juna a zahiri ke nufi waja nesan da suka yi a kishiyantar juna ? yadda za mu iya ba da amsar wannan tamba ya shi ne;            yana da kyau mu kara komawa zuwa ga kur ‘anin kansa domi wasu daga ayoyin wannan saukakken littafi mai girma na fassara junansu kamar yadda muke karantawa daga suratul baiyyinat cewa; “hakika wadannan da kafirta daga cikin ma’abot littafi (wadanda aka saukarwa dalittafi) da mushrikai na cikin wutar jahannama kuma masu dawwama ne a cikinta kuma su ne mafi ashararan mutane (talikai) lallai wadanda sukai imani tare da yin aiki na gari wadannan su ne mafifita alherin mutane (talikai)”[10] daga cin wadannan ayoyi biyu mun samu cewa mutum na da nauo ‘i biyu daga ciki ya kan iya zama mafi kyan halitta kuma mafi girmansu a daraja, da kuma zama mafi munin halitta mafi kaskancinsu a wulakanta, wannan aya ta yi bayanin yadda mutum kan zama mafi daraja a tsakanin sauran halittu, da kuma zama mafi kaskancin halittu, abin nufi mutum ma’abocin imani da yin aiki na gari ya kan zama mafificin halittun Allah a nan duniya, amma idan ya bi hantyar tauri kai, sabo da jayayya ita ce kan fado da shi zawa makaskanciyar daraja har ya zama mafi munin halittun Allah; ya zo daga wasu ruwayoyi cewa, amirul mu’uminin Aliyu dan abi dali amincin Allah ya tabbata a gare shi yana cewa; hakika Allah ya sanyawa mala’iku cikakken hankali babu sha`awa, ya sanyawa dabbobi sha’awa amma babu hankali, sannann ya sanyawa mutum dukkan wadannan abubuwa biyun, duk wanda ya rinjayar da hankalinsa a kan sha’awarsa wannan ya fi mala;ika daraja, wanda kuwa ya rinjayar da son ransa (sha’awarsa) kan hankalinsa to gwara dabba da shi ”[11]. Zamu iya amfana sosai daga wannan ruwaya mai amfani da hikimar gaske kamar; kamar nuna cewa mutum ai halicceshi da bangarori biyu ne (bangaren ransa da kuma bangaren jikinsa) don haka zai iya karkata ne tsakanin bangarori biyu (karkatuwa zuwa bangaransa na samuwa da na jikinsa) tare da ikon zabar wanda ya fi so tsakanin wadannan bangarori wadda dama ce da Allah ya ba shi tare da yancin gudanar da yadda yake sodon haka ne idan ya zabi hanyar aminci da alheri sai samu isa zuwa daukakar da dan Adam ke iya samu ta koli idan kuwa ya zabi da yar sai ya fado zuwa magangara mafi kaskanci kamar yadda Kur’ani yai nuni da shi cewa “wadannan kamar dabbobi ne ko kuma sun fi dabbobin ma lalacewa”[12]. Haka ayoyin kur’ani masu haske suka kara fayyace mana tare da yaye hijabi zuwa sanin hakikanin wannan abu shi ne cewa ko wane daya daga mutane na da dama da ikon samun wannan matsayi mafi girma; daukaka kuma mafi kamalar (cikar) da mala’iku ke iya kaiwa, anan ne matsayin amfani da hankali ke kai nmutum zuwa mafi girman alkhairai ya kai shi zuwa matsayin halifan Allah. Amma idan bai sa kansa da faidantuwa da wannan ludufin Allah ba, bai da damar samun wannan matsayi mai girma wanda Allah ya ba shi tsakanin halittunsa. Daga nan ne mutum ka fadowa zuwa tabewa ya wzama na kasan kaskantattu ya zama abin zargi, tuhuma, da tsawatarwa daga Allah. (duba tafsirul mizaan bol.18 page 527-524)

 


[1] Suratul isra’I aya ta 70

[2] Saratul bakara aaya ta 30

[3] Saratul ahzabi a ya ta 72.

[4] suratu fussilst aya ta 49,50, 51

[5] suratu shura aya ta 27

[6] suratu Ibrahim aya ta 34

[7] suratul ahzab aya ta 72

[8] suratu yasin aya ta 77

[9] suratul asr aya ta 2

[10] suratul bayyinat aya ta 6,7

[11] tafsir nurth thakalaiyn bol.3 page 188

[12] suratul a’araaf aya ta 179

 

TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

  • menene hakikanin ma’anar salla?
    36439 Halayen Aiki 2012/07/25
    Salla daukakace ga duk mai san daukaka, ita ce hanya kai tsaye ba tare da shamaki ba, domin ita ce ganawa da ubangiji. Kamar yadda ya zo a Kur'ani mai girma cewa “hakika ni ne ALLAH wanda ba wani ALLAH sai ni to ku bauta ...
  • mece ce alakar jagorancin malami da jam'iyyu?
    7110 Tsare-tsare 2012/07/24
    Kungiyoyin siyasa, da ma'anar wasu jam'iyyu masu iri-iri akwai su a cikin kowace al'umma tun zamanin da. A yanzu ana ganin jam'iyyun siyasa a matsayin wani abu na tarayyar mutane da 'yancin zabe ne. bisa wannan asasin ne ya zama dole mu kalli wannan lamari a matsayin ...
  • Shin zai yiwu ai mana bayanin tafsirin suratu kausar?
    15332 Tafsiri 2017/06/17
    Suratu kausar sura ce da take da ayoyi guda uku, abin da ya fi shahara gun malamai shi ne an sauke ta a garin makka; sannan dalilin saukar ta shi ne yayewa manzon rahama (s.a.w) damuwar da yake ciki sakamakon mauta da gorin da wasu cikin kuraishawa ...
  • Ta yaya za a magance matsala, idan lamarin na hankali ya ci karon da na addini?
    14504 Sabon Kalam 2012/09/16
    Hankali shi ne hujjar Allah ta addini wacce ya ba wa mutum, hankali ke yi wa mutum jagora har ya kai shi ga samun cikakkiyar kamala, Shari`a hujja ce ta fili wacce take hana mutum gurbata da cutaya kuma ta kai shi ga samun cika da rabauta. ...
  • shin Imamul hujja a tsibirin bamuda yake zaune?
    15739 تاريخ بزرگان 2012/07/25
    Dalilin da ya sa wasu mutane suka yi ammanar cewa “Tsibirin Bamuda shi ne mazaunar Imamu Mahdi (a.s), gani suke Tsibirin Bamuda shi ne “Jazijrayul Khadra’a”. Bisa kaddara cewa Jaziratuk Khadra’a ita ce mazaunar Imamu Mahdi (a.s) shi ya sa suka ce Tsibirin Bamuda ya kunshi wadannan ...
  • Yaya aka samu sauyi a addinin Kiristanci, kuma da wane dalili ne ya samu karkacewa da jirkicewa
    12699 Sabon Kalam 2012/07/23
    Yayin da masu biyayya ga addinin Isa (a.s) suka haramata wa kawukansu wannan ni'ima ta samuwarsa a cikinsu, har ya samu hawa zuwa sama, sai manzanninsa da 'yan sakonsa suka ci gaba d aisar da sakonsa, kuma suka fuskanci wahalhalu masu yawa a kan hakan.
  • An lura da cewa Kur’ani mai girma shi ne mu’ujizar cika makin Manazannin Allah, to meye fuskokin gajiyarwar (kalu balen) da ke akwai a cikinsa?
    16211 Ilimin Kur'ani 2012/07/25
    An ambaci fuskokin gajiyarwar (kalu balen) da Kur’ani mai girma ya yi wadda zai yiwu na ambaci uku daga ciki: Ya gajiyar ta bangaren yare da bayani Ya gajiyar da fuskacin abin da ya kunsa Sannan kuma ya gajiyar ta ...
  • menene dalili a kan tabbatar shugabancin malami.
    18045 Hakoki da Hukuncin Shari'a 2012/07/26
    Akwai hanyoyi mabanbanta domin tabbatar da “shugabancin malami” sai dai a nan za mu isu da ambaton dalilai guda biyu na hankali da na ruwaya domin tabbatar da ita. Dalili na hankali: Hankali ya tabbatar da wajabcin samun mutumin da ke ...
  • Ta wace Hanya ake mangance maita da kanbun baka?
    40482 Halayen Aiki 2017/05/21
    Lalle Alkura'ani ma ya tabbatar da akwai maita, inda ya nuna wasu alamu da suke gaskata abin da tarihi ya tabbatar na daga cikin abin da Al’kur'anin ya zo da shi na daga al’umman da suka shude. Wasu malamai a wannan zamanin suna ganin wasu daga cikin ...
  • Menene hukunchi namijin da ba ya iya biyawa matarsa hakkokinta?
    13746 2019/06/16
    dawwamar rayuwar aure da karfafarta ya dogara da soyayya da kauna da fuskantar juna da girmama juna. Domin iyali su samu tsayuwa da dawwama Addini Muslunci ya sanya hakkoki ga kowanne dayansu ya kuma ayyana musu wajibai a kansu, duk sa”ilin da aka ce akwai hakkoki to ...

Mafi Dubawa